Babban Labari

Yadda muka kashe sabon shugaban ISWAP – Sojoji

Yadda muka kashe sabon shugaban ISWAP – Sojoji

*Su 38 muka halaka a lokaci guda, inji rundunar*Yayin da 1,199 suka tuba Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya ta bayyana cewa, Rundunar Musamman ta Operation Haɗin Kai da ke aikin kawar da ’yan ta’adda a Yankin Arewa Maso Gabas ce ta halaka sabon shugaban Ƙungiyar ISWAP, mai fafutukar yaƙi da kai hare-hare a yankin, wanda aka fi sani da Malam Bako, tare da wasu ’yan ta’addar guda 38. Rundunar Sojojin ta ƙara da cewa, kimanin ’yan fafutukar da iyalansu 1,199 ne su ka tuba,waɗanda suka haɗa da maza 114, mata 312 da kuma yara…
Read More
Dokar kiwo a Kudu: Makiyaya sun fara hijira zuwa Arewa

Dokar kiwo a Kudu: Makiyaya sun fara hijira zuwa Arewa

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Sakamakon sanarwar da mafi yawan gwamnonin kudancin Nijeriya suka bayar na hana Fulani makiyaya gudanar da kiwo a jihohinsu ta sa dubban Fulani yin hijirar dole zuwa Arewa, musamman daga jihohin Oyo, Osun, Ogun, Ondo, Lagos da Ekiti. Wakilin Manhaja a Jihar Jigawa ya gane wa idonsu yadda makiyayan suke tururuwa shiga jihar Jigawa daga jihohin Yarabawa da Igbo bayan da suka yi kiran da su fice su bar mu su yankunansu. Shugaban Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah, reshen Jihar Jigawa, Alhaji Adamu Idris Babura, ya ce, shi da kansa ya gane wa idonsa 'yan…
Read More
An sako ɗalibai 30 da malamai biyu na Kwalejin Yauri

An sako ɗalibai 30 da malamai biyu na Kwalejin Yauri

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Rahotanni daga Jihar Kebbi na bayyana cewa, ɗalibai 30 da kuma  malamai biyu da aka sace daga makarantar Kwalejin Tarayya ta Birnin Yauri sun samu kansu. Kamar yadda wata takarda mai ɗauke da sa hannun Alhaji Yahaya Sarki, Mataimaki na Musamman kan Harkar Yaɗa Labarai ga Gwamna Atiku Bagudu na jihar, ta bayyana cewa, “Yau Alhamis 21 (jiya) ga watan Oktoba, ɗalibai 30 daga makarantar FGC Birnin Yauri sun iso nan babban birnin jiha  bayan da aka sako su. Yanzu haka ana cigaba da duba lafiyarsu kafin a sada su da iyayensu. Haka-zalika yanzu haka gwamnati tana…
Read More
Babbar jikar Sardauna, Hajiya Hadiza Shehu Kangiwa ta rasu

Babbar jikar Sardauna, Hajiya Hadiza Shehu Kangiwa ta rasu

Daga IBRAHEEM HAMZA MNUHAMMAD Allah Ya yi wa Hajiya Hadiza Shehu Kangiwa, babbar jikar jikar Sardauna, Ahmadu Bello rasuwa. Aminiyar marigayiyar, Hajiya Binta Tafawa Balewa ta shaida wa Manhaja cewa, "Hajiya Hadiza Shehu Kangiwa, wacce mata ce ga marigayi tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato ta da, Alhaji Shehu Kangiwa. "Ta kasance babbar jikar marigayi Sardauna Ahmadu Bello, kuma 'yar fari ga Hajiya Inno Ahmadu Bello. "Marigayiyar ita ce 'yar marigayi Wamban Kano, Abubakar Ɗan Maje, kuma babban ɗa ga marigayi Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na 1. "An haife ta ne a shekarar 1960, ta rasu ran Talata a Sakkwato, ta bar…
Read More
EFCC ta yi awon gaba da shugaban KASUPDA yana tsakiyar ganawa da ma’aikata

EFCC ta yi awon gaba da shugaban KASUPDA yana tsakiyar ganawa da ma’aikata

Daga MAHDI M. MUHAMAD a Abuja A ranar Litinin da ta gabata ne Jami'an hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa ta'annati (EFCC), sun cafke shugaban hukumar raya birane na jihar Kaduna (KASUPDA), Malam Ismail Umar Dikko. Shugaban wanda ya yi fice wajen rusa kadarorin jama’a kuma kowa ke shakkansa, an cafke shi ne yayin da yake ganawa da ma'aikatansa. Kafin ya zama shugaban hukumar a 2019, Ismail ya kasance mataimaki na musamman ga gwamna Nasir El-Rufai.Shigowar jami’an EFCC cikin harabar tare da baqar mota ƙirar Hilux Toyota da farko ya haifar da fargaba a tsakanin ma’aikatan, musamman…
Read More
Dokar aika sakamakon zaɓe: Akwai buƙatar jituwa tsakanin majalisa da INEC – Atiku

Dokar aika sakamakon zaɓe: Akwai buƙatar jituwa tsakanin majalisa da INEC – Atiku

Daga MAHDI M. MUHAMAD a Abuja Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar PDP a babban zaɓen 2019, Atiku Abubakar ya yaba da yadda aka warware rashin jituwa tsakanin majalisar ƙasa da hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) kan watsa sakamakon zaɓe ta hanyar Intanet. Wata sanarwa da ofishin yaɗa labarai na tsohon Mataimakin Shugaban ƙasar ya fitar ranar Talata, ya ce, daidaita matsayin tsakanin cibiyoyin biyu wata manuniya ce cewa dimokuraɗiyyar Nijeriya na ci gaba da samun ƙarfi. Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasar ya kuma yaba wa ɗaiɗaiku da ƙungiyoyi musamman ƙungiyoyi daban-daban masu fafutukar kare…
Read More
Shin Gwamna Ganduje ya tsokano tsuliyar dodo?

Shin Gwamna Ganduje ya tsokano tsuliyar dodo?

*Malaman Kano sun yi wancakali da shirin gwamnatinsa na tuge jagoransu*Sanatocin jihar sun yi masa tawaye Daga HAMISU IBRAHIM da AMINA YUSUF ALI a Kano Siyasar Jihar Kano tana da wuyar sha’ani ta fuskar tarihi, inda a mafi yawan lokuta wasu ɓangarori kan zamo silar rugujewar tafiyar ɗan siyasa bisa la’akari da waɗanda suka yi masa taron dangi. Ire-iren waɗannan vangarori sun haɗa da malamai, sarakuna da kuma gidajen siyasar jihar. Ba kasafai wani ɗan siyasa kan yi galaba kan waɗannan sassa ba ko da kuwa shi ke riƙe da madafun ikon jihar a matsayin gwamna. A cikin wannan makon…
Read More
Baya ta haihu kan batun sakin ɗaliban Yawuri

Baya ta haihu kan batun sakin ɗaliban Yawuri

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Ranar Larabar da ta gabata ne labarin sako ɗaliban makarantar Birnin Yauri (Yawuri) ya mamaye kafafen yaɗa labarai bayan da wani ya aika labarin ta yanar gizo, inda ya rubuta kamar haka; “Kimanin ɗalibai da ma’aikata sama da 90 da aka sace a Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke Yawuri a Jihar Kebbi sun shaqi iskar ‘yanci bayan kwanaki 118. Rahotanni daga jihar sun bayyana cewa, mahaifin ɗaya daga cikin ɗaliban da aka kama, wanda bai so a ambaci sunansa, shine ya tabbatarwa da Daily Trust hakan a daren nan, kamar yadda jaridar ta wallafa a…
Read More
Ranar Malamai Ta Duniya: Malamai na cikin wani hali a Kebbi

Ranar Malamai Ta Duniya: Malamai na cikin wani hali a Kebbi

Daga Jamil Gulma a Kebbi Ranar ranar 5 ga Oktoba na kowacce shekara aka tsayar a matsayin Ranar Malamai ta Duniya, inda a wurare daban-daban na faɗin duniya ake gudanar da bukukuwa da taruka da kuma lakcoci dangane da abin da ya shafi aikin koyarwa, inda a waɗansu wuraren har ma akan karrama waɗansu haziƙan malamai da suka cancanta. Nijeriya ma ba a bar ta a baya ba wajen murnar zagayowar wannan ranar, sai dai ba wani abu na a-zo-a-gani da ake ganin an aiwatar bayan ranar ba a karatu illa malamai da ɗalibai suna zaune a gida. Wakilin Manhaja…
Read More
Shugaban malaman makaranta na Nijeriya ya bayyana dalilan rashin ingancin ilimi

Shugaban malaman makaranta na Nijeriya ya bayyana dalilan rashin ingancin ilimi

Daga AMINU AMANAWA a Sokoto Shugaban Ƙungiyar Malamai ta Ƙasa, Kwamred Nasir Idris, ya bayyana matsalar tsaro a makarantu, rashin aiwatar da mafi ƙankantar albashi ga ma’aikata da ma ƙarancin malamai a makarantu a matsayin wasu daga cikin ƙalubalan da ke cigaba da zama tarnaƙi ga malamai da ma ɓangaren ilimi ɗungurugum a Nijeriya. Dr Nasir Idris ya dai bayyana hakan ne a cikin wani bayani da ya fitar, domin Bikin Ranar Malamai ta wannan shekarar, yayin da shugaban ƙungiyar malamai ta Jihar Sokoto, Kwamred Umar Moyi Tambuwal, ya gabatar a wajen taron da aka gudanar a makon nan a Sokoto,…
Read More