Babban Labari

Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Ƙungiyar Kare 'Yancin Zamantakewa Da Yaƙi Da Cin Hanci (SERAP), ta yi kira ga Shugaban Majalisar Dattawa Dr Ahmad Lawan, da takwaransa na Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Femi Gbajabiamila, a kan su buƙaci hukumomin yaƙi da rashawa su binciki badaƙalar ɓatan dabon da kasafin biliyan N4.4 na Majalisar Tarayya ya yi kamar yadda rahotannin binciken ofishin Babban Jami'in Bincike na Ƙasa suka nuna. A wata wasiƙa da ta samu sa hannun mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ƙungiyar ta ce, "Ta hanyar kwatanta jagoranci nagari a kan wannan batu, Majalisar Tarayya za ta iya nuna wa 'yan Nijeriya cewa ɓangaren yin…
Read More
Yaƙi Da Matsalar Tsaro: Zulum ya ƙalubalanci shugabannin tsaro su kyautata alaƙa da takwarorinsu

Yaƙi Da Matsalar Tsaro: Zulum ya ƙalubalanci shugabannin tsaro su kyautata alaƙa da takwarorinsu

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Barno, Babagana Umara Zulum, ya ƙalubalanci sabbin shugabannin tsaro da su assasa kyakkyawar alaƙar aiki a tsakaninsu da ƙasashen da Nijeriya ke maƙwabtaka da su, wato Chadi da Kamaru da kuma Nijar. Kazalika, ya shawarci manyan hafsoshin da su kasance masu haƙuri da kuma sauraron jama'a a halin aiwatar da ayyukansu. Gwaman ya faɗa wa jami'an haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncinsu a fadar gwamnatin jihar a Lahadin da ta gabata yayin da suka yi ziyarar aiki ta farko a jihar. Shugaban tsaro Major-General Leo Irabor, shi ne ya jagoranci takwarorinsa Major-General Ibrahim Attahiru…
Read More
Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Daga FATUHU MUSTAPHA A ranar Asabar da ta gabata Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama cikakken dan jam'iyyarsu ta APC, a mahaifarsa Daura da ke jihar Katsina. Tare da kira ga daukacin shugabannin jam'iyyar da karfafa kwazo wajen tabbatar da APC ta samu karin tagomashi a matakin farko. Buhari ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karbi bakuncin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Lawan da wasu gwamnoni hada da wasu 'ya'yan jam'iyyar APC a garin Daura, jim kadan bayan ya kammala sabunta rijistarsa ta jam'iyya a Gundumar Sarkin Yara. A wata sanarwa da mai magana…
Read More
Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, rattaba hannu da ya yi a dokar Budaddiyar Jami'ar Nijeriya (NOUN) da aka yi wa gyaran fuska, ya haifar wa jami'ar da ɗalibanta samun tagomashi a kasa. Shugaban ya bayyana haka ne yayin bikin yaye daliban jami'ar karo na 9 da na 10 da aka hade wuri guda wanda ya gudana ta bidiyo a ranar Asabar da ta gabata. Da yake jawabi yayin bikin ta bakin wakilinsa Mataimakin Sakataren Hukumar Kula da Jami'o'i ta Kasa, Ramon Yusuf, Buhari ya ce, "Budaddiyar Jami'ar tana sauke nauyin da ya rataya a kanta…
Read More
Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Daga WAKILINMU Hukumar Birnin Tarayya, Abuja ta ce, za ta tabbatar da an bi dokokin yaki da Cutar Korona na 2021 kamar yadda Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da Cutar Korona ya shimfida. Hukumar ta bayyana haka ne a wajen wani taron masu fada a ji da ya gudana a karkashin jagorancin Ministan Abuja, Malam Muhammad Musa Bello, a Juma'ar da ta gabata a Abuja. Da yake jawabi yayin taron, Ministan Abuja ya ce, "Za a kara himma wajen wayar da kan mazauna Abuja game da kiyaye dokokin yaki da Cutar Korona, tare da tabbatar da an hukunta duk wanda…
Read More
Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Daga UMAR M. GOMBE Cibiyar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ta bayyana cewa, an samu rasuwar mutum 27 cikin sa'o'i 24 a fadin kasa sakamakon Cutar Korona. Cibiyar ta sanar da hakan ne a shafinta na intanet a Juma'ar da ta gabata, inda ta ce kawo yanzu adadin wadanda suka mutu a fadin kasa a dalilin korona ya cilla zuwa mutum 1,557. Kazalika, NCDC ta sanar an samu karin mutum 1,114 da suka harbu da cutar ta korona a fadin kasa. Wanda a cewarta, "Ya zuwa yanzu mutum 128,674 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a fadin kasa."…
Read More
Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Adaga FATUHU MUSTAPHA Fadar Shugaban Kasa ta sanar cewa sabbin shugabannin sojojin da aka nada kwanan nan za su bayyana gaban Majalisar Dattawa domin tabbatar da nadin nasu. A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a, Hadimin Shugaba Buhari Kan Harkokin Majalisar Tarayya (Bangaren Dattawa), Sanata Babajide Omoworare ya bayyana cewa, tuni Shugaba Buhari ya tura wasika ga Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, yana mai bukatar a tabbatar da nadin wadanda lamarin ya shafa. Sanarwar ta nuna cewa: “Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar da Majalisar Tarayya nadin da ya yi tare da neman majalisar ta tabbatar da nadin nasa…
Read More
Kiris ya rage Obasanjo ya yi mini ritaya daga aiki – Buratai

Kiris ya rage Obasanjo ya yi mini ritaya daga aiki – Buratai

Daga UMAR M. GOMBE Tsohon shugaban rundunar sojan Nijeriya, Lt. Gen. Tukur Buratai, ya bayyana cewa, kiris ya rage tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya yi masa ritaya daga aikin soja shekaru 21 da suka gabata. Ya ce, wannan ya faru ne a lokacin yana matsayin Manjo, tare da bayyana samun zarafin kaiwa matsayin 'Lieutenant General' da kuma Babban Hafsan Hafsoshi da ya yi a matsayin al'amari da ya shiga tarihi. Buratai, ya yi wadannan bayanan ne yayin da yake jawabin bankwana wajen mika ragamar aiki ga magajinsa Maj. Gen. Ibrahim Attahiru a babban ofishin sojoji da ke Abuja a…
Read More
Inganta fannin lafiya shi ya fi muhimmanci ga Nijeriya bisa ga sayo rigakafin korona – Gates

Inganta fannin lafiya shi ya fi muhimmanci ga Nijeriya bisa ga sayo rigakafin korona – Gates

Daga FATUHU MUSTAPHA Hamshakin dan kasuwar nan na Kasar Amurka, Bill Gates, ya shawarci Nijeriya da ta karkatar da hankalinta zuwa ga inganta fannin lafiyarta maimakon kashe makudan kudade wajen sayo allurar rigakafin cutar korona. Gates ya ba da shawar ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai ta bidiyo a Talatar da ta gabata, inda ya yi kira ga Nijeriya da kada ta yi amfani da 'yan kudaden da ta ware don kula da fannin lafiyarta wajen sayen rigakafin COVID-19 mai tsadar gaske. Jaridar Manhaja ta kalato dan kasuwar na cewa, “Ina mai bada shawarar a bai wa…
Read More
Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Daga AISHA ASAS, Abuja Gwamnatin Tarayya ta ce, ana sa ran a soma allurar rigakafin cutar korona ya zuwa karshen Maris ko Afrilun 2021.Ministan Lafiya, Osagie Ehanire ne ya bayyana haka sa'ilin da Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da COVID-19 (PTF) ke gabatar da bayanin ayyukankasa, Litinin da ta gabata a Abuja. Ehanire ya ce, "Adadin maganin da Nijeriya ta yi odar sa ta AVATT na Hukumar Hada Kan Afirka, ya danganci daidai adadin da ake bukata ne don gundun barna." Ya ci gaba da cewa, Nijeriya na yin dukkan maiyiwuwa don tabbatar da an yi wa akalla kashi 70…
Read More