Babban Labari

Me ke wahalar da Ganduje a kotu?

Me ke wahalar da Ganduje a kotu?

*Cikin shari’u huɗu an kayar da shi uku*Shin ko dai tsiyar nasara sai za shi gida ne? Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A cikin shari’u guda huɗu mafi shahara da Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yi a gaban kotuna, sau ɗaya kawai ya yi nasara, inda ya sha kayi a guda uku. Shari’ar da ya yi nasara ita ce wacce ya kara da ɗan takarar PDP a zaɓen 2019, Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-gida), amma dukkan ukun da suka biyo bayan wannan shine ya kai ƙasa. Sauran shari’un uku su ne, na rikicin gwamnan da Mawallafin…
Read More
Ƙarin kuɗin mai: Cikin ’yan Nijeriya ya ɗuri ruwa

Ƙarin kuɗin mai: Cikin ’yan Nijeriya ya ɗuri ruwa

*Fetur na iya tashi zuwa Naira 340 lita guda – Shugaban NNPC*Za mu ba da tallafin sufurin Naira 5,000 duk wata, inji gwamnati*Babu tanadi a kasafin 2022 – Majalisar Dattawa*Matakin zai haifar da cin hanci da rashawa – Masu ruwa da tsaki*Yadda NNPC ke kashe Naira tiriliyan 1.8 akan tallafi duk shekara Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Cikin mafi yawan ’yan Nijeriya ya ɗuri ruwa kan makomarsu muddin cire tallafin man fetur bakiɗaya ya kankama nan da watanni. Tun bayan samun sanarwar daga Gwamnatin Tarayya da ke tabbatar da cewa, a watannin farko na shekarar 2022 za a cire…
Read More
Zaɓen Anambara: Ba lallai a rantsar da Soludo a matsayin gwamna ba

Zaɓen Anambara: Ba lallai a rantsar da Soludo a matsayin gwamna ba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Bincike a jihar Anambra da ke Kudu maso Gabashin Nijeriya, inda aka gudanar da zaɓe kwanan nan, kuma tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya, Farfesa Charles Chukwuma Soludo, ya zama wanda ya lashe zaɓen, ya bankaɗo wani babban batu, wanda fitaccen masanin tattalin arziki kuma ma'aikacin banki ya aikata. Wani bincike ya nuna cewa, ɗan takarar jam'iyyar PDP, Valentine Ozigbo wanda ya zo na biyu a zaɓen gwamnan jihar Anambra a ranar 6 ga Nuwamba, 2021, ana iya rantsar da shi a matsayin zaɓaɓɓen gwamnan jihar Anambra na gaba. Ta kuma bayyana cewa, Farfesa Charles Soludo, na…
Read More
Tubabbun ‘yan Boko Haram sun yi zanga-zanga kan rashin cin nama

Tubabbun ‘yan Boko Haram sun yi zanga-zanga kan rashin cin nama

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ɗaruruwan 'yan Boko Haram da ke a sansanin da aka killace su bayan da suka miƙa wuya ga sojojin Nijeriya sun tayar da tarzoma a ranar Laraba da nufin gwamnatin ta dinga yanka musu shanun da ake kawo musu. Tarzoma ta tayar da hankalun mazauna garin Maiduguri da ke kusa da sansanin tubabbun mayaƙan na Boko Haram, inda mazauna garin suka ɗauko adduna, takobi da kuma gariyo suna barazarar kashe duk ɗan Boko Haram ɗin da ya yi yunƙurin barin sansanin, a cewar majiyar da ta shaida wa kafar AFP. Lamarin ya nuna yadda…
Read More
Tattalin arziki da tsaro: Nijeriya ta samu tagomashi da koma-baya

Tattalin arziki da tsaro: Nijeriya ta samu tagomashi da koma-baya

*Hauhawar farashi zai jefa ’yan Nijeriya miliyan shida cikin talauci – Bankin duniya *Fyaɗe 11,200 aka yi a Nijeriya daga bara zuwa bana – Amnesty International *Tattalin arzikin Nijeriya ya ƙaru da kashi 4.03 a 2021 – NBS *Yanzu babu tursasawar addini a Nijeriya – Amurka Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Daga dukkan alamu al’amuran Nijeriya su na yin kwangaba-kwanbaya ko kuma a ce tafiyar kura, inda yayin da a wani fannin ta samu cigaba, a wani fannin kuma ci-baya ta samu. Ga yadda Manhaja ta haɗo muku rahotanni kan halin da ƙasar ke ciki, musamman ma a wannan…
Read More
Ƙarya ta ƙare kan batun Mambila!

Ƙarya ta ƙare kan batun Mambila!

*Babu sauran tarnaƙi tunda Kamfanin Sunrise ya janye ƙararsa – Malami*Gwamnati na iya yin sulhu da Kanu da Igboho, inji Ministan Shari’ar Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ministan shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya), Abubakar Malami, ya bayyana cewa, kamfanin samar da wutar lantarki na ‘Sunrise Power Transmission Company of Nigeria Ltd’ (SPTCL) ya watsar da shari’ar da ya ke yi wa Gwamnatin Nijeriya, lamarin da ya kai ga kawo jinkiri ga aikin samar da wutar lantarki na Mambilla, yana mai cewa, a yanzu hakan na nuni kenan da babu sauran tarnaƙi wajen cigaba da aikin samar da wutar lantarki da…
Read More
Dokar mai: Yadda cacar baki ta kaure a majalisa kan Bauchi, Legas da Ogun

Dokar mai: Yadda cacar baki ta kaure a majalisa kan Bauchi, Legas da Ogun

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Yayin zaman Majalisar Dattawa na jiya Alhamis, wata 'yar hayaniya ta kaure yayin da aka gabatar da dokar da za ta saka wasu jihohi uku a jerin masu fitar da man fetur a Nijeriya, a cikin garambawul ɗin da ake yi wa Hukumar NDDC. Sanata Adeola daga jihar Legas, shi ne ya gabatar da ƙudirin wanda ya ƙunshi saka jihohin Bauchi, Legas da Ogun cikin jerin jihohi masu samar da albarkatun man fetur ɗin, sai dai lamarin bai wa sanatocin da suka fito daga yankin Neja Delta daɗi ba, inda suka yi fatali da…
Read More
Buhari ya taya ɗan uwansa, amininsa Mamman Daura, murnar zagayowar ranar haihuwarsa

Buhari ya taya ɗan uwansa, amininsa Mamman Daura, murnar zagayowar ranar haihuwarsa

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Shugaban Nijeyiya Muhammadu Buhari ya taya Malam Mamman Daura murna cikar sa shekaru 82 da haihuwa ranar 9 ga watan Nuwamba, 2021. Cikin saƙon shugaban ga ɗan uwan nasa kuma mafi kusanci da shi, wanda mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Malam Garba Shehu, ya sanya wa hannu a Abuja, Shugaba Buhari ya ce, “babu wanda ya fi dacewa da na taya shi murnar zagowar ranar haihuwa, kamar Malam Mamman Daura." Sannan ya bayyana shi a matsayin "mutum mai cikar nagarta, wanda da dama ake mutuntawa kan yadda ya nemi ilimi kuma ya…
Read More
Hankalin ‘yan siyasa ya raja’a ga zaɓen gobe na Anambra

Hankalin ‘yan siyasa ya raja’a ga zaɓen gobe na Anambra

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Zuwa yanzu dai hankalin kowane ɗan siyasa da masu fashin baƙi akan al'amuranta ya koma kan zaɓen gwamnan Jihar Anambra, tun bayan da jam'iyyar PDP ta gudanar da babban taron ta a Asabar da Lahadin makon jiya a Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda mutane da dama, ciki har da jam'iyya mai mulki ke musu shaguɓe da habaicin taron ba zai yiwu ba, saboda rikice-rikicen da ke cikin gidan jam'iyyar. Me ya yi saura yanzu? Sai zaɓen jihar Anambra, wanda shi ne madubi a wajen 'yan siyasa a cikin satin nan, wanda kuma ma tun…
Read More