29
Jan
*NNPC na buƙatar Naira tiriliyan uku a 2022 Daga MAHDI M. MUHAMMAD da SANI AHMAD GIWA a Abuja A ƙarshe dai Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari na Nijeriya ta yi watsi da cece-kucen da ake yi na buƙatar ko akasin haka wajen cire tallafin man fetur, inda ta ce, ta bar zaɓin aiwatar da hakan ga wanda zai gaji ofishin Shugaban Ƙasa a 2023, saboda yanayin halin da tattalin arzikin Nijeriya da ma na ’yan Nijeriya ke ciki a halin yanzu. Kana kuma, idan shawarar ta wuce gaban Majalisar Dokoki ta ƙasa da ake sa ran za ta ba ta wasu…
