27
Feb
*Shin gaba Sanata Nasiha ya ci ko kuwa baya? Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Daga dukkan alamu siyasar Jihar Zamfara na cigaba da zama wahainiyar da ke rikiɗa tana yin juyin wainar da ba a saba gani ba a tarihin siyasar Nijeriya bakiɗaya. Idan za a iya tunawa, a shekara ta 2019 kwana ɗaya kafin rantsar da sabuwar gwamnati ne bakiɗayan waɗanda aka zaɓa a tutar ƙarƙashin Jam’iyyar APC a jihar, Kotun Ƙolin Nijeriya ta kore su a yayin da ta yanke hukuncin da ya ɗora ilahirin ’yan takarar Jam’iyyar PDP, waɗanda bakiɗayansu sun faɗi zaɓe a lokacin da aka…
