06
Mar
DAGA MUHAMMADU MUJITABA Shugaban Ƙungiyar Malaman Sakandire ta Ƙasa reshen Jihar Kano (ASUSS), Kwamared Abdu Usman Yalo ya ce su malaman sakandire na Jihar Kano ba su da matsalar biyan albashi daga gwamnatin Kano ko matsalar rashin ƙarin girma, ya ce duk wata ana biyan su albashi tun tsohuwar gwamnati har zuwa gwamnatin Dr. Abdullahi Umar Ganduje ba su da matsalar rashin biyan albashi kamar yadda wasu jihohin ƙasar nan ke fuskantar matsala. Usman ya ƙara da cewa "ƙarin girma shi ma ba mu da matsala ana yi kamar yadda ya ke a ƙa`ida sau biyu a shekara, ana mana…
