Babban Labari

Gwamnatin Tarayya na shirin cire dokokin kariyar Korona

Gwamnatin Tarayya na shirin cire dokokin kariyar Korona

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta bayyana cire dokar da ta wajabta amfani da takunkumin baki a wajen mu'amalar jama'a da wuraren taruka da ofisoshi, don hana yaɗuwar annobar Korona. Kwamitin Shugaban Ƙasa na Covid-19 wanda Sakaten Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha ke jagoranta, shi ne ya sanar da hakan, inda ya bayyana cewa saka takunkumin a wuraren taron jama'a zai kasance zaɓi ga wanda ke buƙata, sai dai kuma dokar za ta fara ne bayan hutun Easter. Yawancin ƙasashe a duniya da dama sun sassauta yawancin dokar kariya da annobar Korona bayan karɓar allurar rigakafin cutar.…
Read More
“Darul Islam ke da alhaki harin jirgin ƙasa”

“Darul Islam ke da alhaki harin jirgin ƙasa”

Daga IBRAHIM HAMZA MUHAMMAD A Janairun bara, Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya bayyana cewa, wata ƙungiya Ansarul Islam, wadda ke da kamanceceniya da Ƙungiyar Boko Haram sun kafa ƙungiyoyi a jihar. Ya ce, "da yawan mambobin ƙungiyar Darul Islam da ke da alaƙa da Boko Haram ɗin, a yanzu sun karkasu wurare biyar a cikin ƙananan hukumomi 13 da ke yankin. "Yankunan sune: Nasarawa, Awe, Doma, Wamba da kuma yankin Karu. Wanda ya haddasa matsalar tsaro a jihar kamar yadda ake samun sabbin hare-hare bayan da jami'an tsaro suka fatattake su kwanan nan." Haka zalika, yayin da jami'an…
Read More
Gidauniyar Bintaliya ta bada tallafin azumi a Kaduna

Gidauniyar Bintaliya ta bada tallafin azumi a Kaduna

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Alhamis ne gidauniyar Bintaliya, wata gidauniya da ta yi fice wajen tallafa wa al'umma masu ƙaramin ƙarfi, ta raba wa dubun-dubatar al'umma kayan abincin azumin watan Ramadan a Jihar Kaduna. An gudanar da taron ne a ɗakin taro na Arewa House da ke Kaduna. Gidauniya ta bayar da irin nata tallafin ga al’umma ne musamman Waɗanda ke buƙatar taimako a garin Kaduna, inda ta ba wa dubun-dubatar al'umma tallafin kayan abinci da suka haɗa da shinkafa, taliya, maggi, Makaroni, gishiri, wanda al'umma da dama su ka amfana. Wakilinmu da ya shaidi rabon waɗannan kaya,…
Read More
Shugabancin APC: Yadda Abdullahi Adamu ya yi fintinkau

Shugabancin APC: Yadda Abdullahi Adamu ya yi fintinkau

*Abinda ya sa gwamnoni na miƙa wuya gare shi – Gwamnan Nasarawa Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Gwamnan Jihar Nasarawa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da tsare-tsare a taron Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi A. Sule, ya bayyana dalilin da ya sa gwamnonin jam’iyyar suka amince wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kan zaɓar tsohon gwamnan Jihar Nasarawa, Sanata Abdullahi Adamu a matsayin shugaba na gaba na jam'iyya mai mulki. A ranar gobe Asabar ne dai aka shirya gudanar da taron a Abuja. Da ya ke zantawa da manema labarai kan shirye-shiryen kwamitinsa gabanin zaɓen, Gwamna Sule, ya ce, waɗanda…
Read More
Taron APC: Yadda takarar Sanata Abdullahi Adamu ke samun tagomashi

Taron APC: Yadda takarar Sanata Abdullahi Adamu ke samun tagomashi

Daga BASHIR ISAH da MAHDI M. MUHAMMAD Yayin da ake dab da gudanar da Babban Taron Jam'iyyar APC na Ƙasa daga dukkan alamu takarar neman kujerar Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa da tsohon Gwamnan Jihar Nasarawa, Sanata Abdullahi Adamu, ke yi ya samu tagomashi mai tarin yawa bisa la’akari da yadda ya ke samun goyon bayan masu ruwa da tsaki a jam’iyyar. Gwamnonin jami’yyar sun yi mubaya’a ga ɗan takarar da Shugaba Buhari ke ra’ayin ya zama shugaban APC na ƙasa, wato Sanata Adamu (Turakin Keffi). Da ya ke magana da manema labarai jim kaɗan bayan kammala taronsu da Shugaba Buhari…
Read More
Ricikin basasar APC:Yadda Buhari ya ƙwaci Buni daga hannun gwamnoni

Ricikin basasar APC:Yadda Buhari ya ƙwaci Buni daga hannun gwamnoni

*Buni ya yi amai ya lashe kan hukunce-hukuncen Gwamna Bello Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya taka wata muhimmiyar rawa wajen ƙwato jam’iyyar APC daga hannun wasu daga cikin gwamnnoninta kuma ya saka damƙa ta a hannun halastaccen Shugaban Riƙo na Jam’iyyar, Mai Mala Buni, bayan da Shugaban Ƙasar ya ƙi goyuwa da bayan juyin mulkin da aka shirya wa Gwamnan na Jihar Yobe. Idan za a iya tunawa, a makonnin biyu da suka gabata a ka ji kuma a ka yarda da cewa, Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta shiga rikicin…
Read More
Tir da kashe ’yan sintiri 63 a Kebbi – Buhari

Tir da kashe ’yan sintiri 63 a Kebbi – Buhari

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana matuqar baƙin cikinsa kan kisan ’yan sintiri su guda 63 da ’yan ta’adda suka yi a garin Zuru na Jihar Kebbi, ya kuma yi kira ga jami’an tsaron mu da su tashi tsaye wajen ganin an shawo kan lamarin. Ya kuma bayyana kisan gillar da wasu ’yan bindiga suka yi wa gomman ’yan sintiri a jihar Kebbi inda suka musu ƙwanton ɓauna a ƙaramar hukumar Sakaba/Wassagu a matsayin abin takaici da ban tausayi. A cewarsa, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Malam Garba Shehu ya fitar, “wannan…
Read More
Shugabancin APC: Musayar yawu ta ɓarke tsakanin El-Rufai da Buni

Shugabancin APC: Musayar yawu ta ɓarke tsakanin El-Rufai da Buni

*Buhari da gwamnoni 19 ne suka kori Buni, inji El-Rufai*Da kaina na sauka don zuwa Dubai neman lafiya, cewar Buni*Babban Taron APC ba gudu ba ja da baya – Gwamna Sani Bello Daga SANI AHMAD GIWA da MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Rikicin da ya ɓarke a jam'iyyar APC ya ɗauki sabon salo yayin da Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya bayyana cewa, shugaba Buhari ya kori Gwamna Mai Mala Buni daga shugabancin jam’iyya, inda daga baya Mai Mala Buni ya fitar da wata wasiƙa da ke nuna kalaman Gwamna Nasir El-Rufa'I ba daidai ba ne. Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir…
Read More
Ranar Mata: Za mu inganta muradun mata – Shugaban INEC

Ranar Mata: Za mu inganta muradun mata – Shugaban INEC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce, za ta cigaba da inganta muradun mata tare da yin haɗin gwiwa da su, domin gudanar da sahihin zaɓe na gaskiya da adalci a siyasance. Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan alƙawarin a cikin wata sanarwa ranar Talata a Abuja, don bikin Ranar Mata ta Duniya. Yakubu ya ce, hukumar ta daɗe tana neman duk jam’iyyun siyasa da suka yi rajista, don inganta damar samun dama ga mata zuwa muƙaman zaɓe. “INEC ta haɗa kai da miliyoyin matan Nijeriya…
Read More
Ahir ɗinku da tsoma hannu a zaɓen 2023 – Janar Yahaya ga sojoji

Ahir ɗinku da tsoma hannu a zaɓen 2023 – Janar Yahaya ga sojoji

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Nijeriya, Laftanar Janar Faruk Yahaya, ya ja kunnen manya da ƙananan hafsoshin sojan ƙasa na Nijeriya da su cigaba da kasancewa ba tare da nuna ɓangaranci ba wajen gudanar da ayyukansu a lokaci da kuma bayan zaɓen 2023. Janar Yahaya ya bayar da wannan umarni ne a taron ƙara wa juna na yini biyu kan Tsarin Aiki da Gudanarwa na hafsoshin sojojin Nijeriya, wanda sakataren ma’aikatar soji ta shirya a ranar Talata a Abuja. Babban Hafsan, wanda ya samu wakilcin shugaban Kawo Canje-canje da Ƙirƙire-ƙirƙire, Maanji Janar Charles Ofoche, ya ce,…
Read More