01
May
•Za su kai hari a masallatai da wuraren shaƙatawa Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A daidai lokacin da ya rage kwana kaɗan al'ummar Musulmi su gudanar da shagulgulan bikin Ƙaramar Sallah a Nijeriya, Hukumar 'Yan Sandan Farin Kaya (DSS) ta ankarar da 'yan Nijeriya kan wani makirci da suka gano da wasu ɓatagari ke shirin aikatawa a lokacin bukukuwan sallah da bayan sallah. Hukumar DSS ɗin da kanta ta ce ta gano cewa, wasu miyagu suna haɗin gwiwa domin saka bama-bamai a wuraren ibada, wuraren shaƙatawa da wasu gine-gine masu muhimmanci yayin bikin sallah. Don haka hukumar ta buƙaci…
