Babban Labari

2023: Ina fata a samu shugabannin da suka fi mu – Masari

2023: Ina fata a samu shugabannin da suka fi mu – Masari

*Ya buƙaci ’yan takara su cire gaba a tafiyar siyasa Daga UMAR GARBA a Kataina Duba da ƙalubalen da Nijeriya ke fuskanta a fannoni daban-daban, kama daga ɓangaren tsaro, tattalin arziƙi, ilimi da dai sauran ɓangororin da za su haɓaka cigaban Nijeriya, Gwamnan Jihar Katsina, Rt. Hon. Aminu Bello Masari, ya yi fatan samun shugabanni waɗanda za su yi aiki fiye da su bayan kammala manyan zaɓukan da suke tafe na shekara ta 2023 lokacin da wa'adin mulkin zaɓaɓɓun masu riƙe da madafun ikon ƙasar ke ƙarewa. Gwamna Masari ya bayyana cewar, ƙasar na buƙatar shugabannin da za su yi…
Read More
Bayyana ra’ayin takara: ’Yan Nijeriya na kira ga Buhari da ya tsige gwamnan CBN

Bayyana ra’ayin takara: ’Yan Nijeriya na kira ga Buhari da ya tsige gwamnan CBN

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An buƙaci shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da ya kori gwamnan babban bankin Nijeriya, Godwin Emefiele daga muƙaminsa kan nuna ra'ayinsa na tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023. Idan za a iya tuna cewa, Emefiele wanda ya sha musanta burin zama shugaban Nijeriya a 2023, ya zaɓi fom ɗin tsayawa takara a ranar Juma'a. Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnan babban bankin na CBN ya karɓi fom ɗin Naira miliyan 100 daga hannun sakataren jam’iyyar na ƙasa (ICC) da ke Abuja. ’Yan Nijeriya da suka mayar da martani kan wannan lamari sun ce ba bisa ƙa’ida ba…
Read More
Osinbanjo da Tinubu sun yi musabiha a taron fitar da ɗan takarar APC a yankin Yarabawa

Osinbanjo da Tinubu sun yi musabiha a taron fitar da ɗan takarar APC a yankin Yarabawa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Karon farko tun bayan ayyana aniyar taka takarar kujeran Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya yi ido huɗu da jagoran Jam'iyyar APC kuma maigidansa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a jihar Legas. Jiga-jigan Jam'iyyar APCn biyu sun haɗu ne yayin wani taron zaman haɗin kai tsakanin 'yan takarar kujerar shugaban ƙasa ƙarƙashin Jam'iyyar APC daga yankin ƙabilar Yoruba. Dattawan yankin Kudu maso Yamma ne suka shirya zaman don ganin yadda za a haɗa kai da juna don tsayar da mutum guda cikinsu. Dattawan sun haɗa da tsohon gwamnan jihar Osun, Cif Bisi Akande, da tsohon…
Read More
Shugaban Bankin CBN ya shiga jerin masu zawarcin shugabancin Nijeriya

Shugaban Bankin CBN ya shiga jerin masu zawarcin shugabancin Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Tuni Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emiefele ya shigo sahun masu zawarcin kujerar Shugaban Ƙasa ƙarkashin tutar APC bayan da shi ma ya yanki takardar bayyana aniyar takara kan miliyan N100. A ranar Juma'a Emiefele ya yankin fom ɗin nasa Tun a 2014 tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan ya naɗa Emiefele Gwamnan Babban Bankin Nijeriya bayan da ya sauke Sunusi Lamido Sunusi.
Read More
Da ɗumi-ɗumi: Rikicin APC a Kano, Shekarau ya sha kaye a hannun Ganduje a kotu

Da ɗumi-ɗumi: Rikicin APC a Kano, Shekarau ya sha kaye a hannun Ganduje a kotu

A ranar Juma'a Kotun Ƙoli ta kori ƙarar da tsagin tsohon Gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau ya shigar yana mai neman kotu ta tabbatar da shi a matsayin halastaccen APC na jihar Kano bisa ga tsagin Gwamna Abdullahi Ganduje. Kotun ta ce ƙarar da ɓangaren Shekarau ya shigar ba ta da hurumin da kotu za ta saurare ta, don haka ta kori ƙarar sannan ta tabbatar da tsagin Gwamna Ganduje a matsayin halastaccen APC a Kano. Cikkaken labari na nan tafe....
Read More
Buhari ya karɓi baƙuncin Guterres a fadarsa

Buhari ya karɓi baƙuncin Guterres a fadarsa

Daga BASHIR ISAH A ranar Laraba Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya karɓi baƙuncin Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Bayanai daga Fadar sun nuna Buhari ya yi ganawar sirri tare da baƙon nasa inda suka tattauna batutuwa da suka shafi Nijeriya, Afirka da sauransu. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Guterres ya zo ziyarar aiki ne na kwana biyu a Nijeriya, inda a ranar Talata ya ziyarci Maiduguri babban birnin Jihar Borno ya gana da waɗanda rikicin ta'addanci ya shafa da kuma mayaƙan Boko Harama da suka ajiye makaminsu.…
Read More
Soja ya kashe kansa bayan ya shiga hannu kan taimaka wa ISWAP

Soja ya kashe kansa bayan ya shiga hannu kan taimaka wa ISWAP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rahotanni daga yankin Arewa maso gabashin Nijeriya na cewa wani sojan ƙasar ya kashe kansa bayan da aka kama shi bisa zargin aiki tare da mayaƙa masu iƙirarin jihadi na ƙungiyar ISWAP. Wakilin BBC ya ce wata majiya mai kusanci da rundunar sojojin Nijeriya ta sanar da shi cewa lallai sojan na da hannu a wasu hare-hare da aka kai kan wasu al'umomin Jiihar Yobe a cikin makonnin da suka gabata. Manyan hafsoshin sojin ƙasar sun fara sa ido kan sojan ne bayan da aka kai wasu hare-hare biyu a garuruwan Geidam da Gashua…
Read More
Gwamnatin Kano ta sha alwashinn cigaba da inganta tsaron jihar

Gwamnatin Kano ta sha alwashinn cigaba da inganta tsaron jihar

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Muƙaddashin Gwamnan Jihar Kano Dr. Nasir Yusuf Gawuna ya jaddada ƙudirin gwamnatin Kano na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al'umma. Gawuna ya bayyana hakan ne a ranar Litinin, ya yin da tawagar ƙwararru akan tsaro daga makarantar samar da tsaro ta ƙasa ta kai masa ziyara a fadar gwamnatin  Kano. Ya bayyana cewa a ƙoƙarin gwamnatin Kano na inganta tsaro ta faɗaɗa majalisar tsaron ta wajen shigo da hukumomin tsaro da kiran mitin akai-akai don samar da yanayi mai kyau a jiha. "Kun zo Kano, ɗaya daga  cikin jihohi mafi zaman lafiya a Nijeriya,…
Read More
Malagi ya sayi fom na tsaya wa takarar Gwamnan Jihar Neja

Malagi ya sayi fom na tsaya wa takarar Gwamnan Jihar Neja

Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Shugaban rukunin kamfanin jaridun Blueprint da Manhaja kuma mai neman tsaya wa takarar gwamna na kan gaba ƙarƙashin Jam’iyyar APC mai mulkin Jihar Neja, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya zavi jam’iyyar inda ya sayi fom na nuna sha’awa da tsayawa takara a zaɓen gwamna a jihar Neja a zaɓen 2023 mai zuwa. Malagi ya biya Naira miliyan 50 na duka fom na nuna sha’awa da na takara a ranar Laraba a sakatariyar jam’iyyar APC ta ƙasa da aka fi sani da gidan Muhammadu Buhari da ke Abuja. Sakataren Ƙungiyar Kamfen ɗin Malagi, Barista Bala…
Read More
’Yan bindiga sun yi garkuwa da Maigarin Rijana

’Yan bindiga sun yi garkuwa da Maigarin Rijana

Daga IBRAHIM HAMZA MUHAMMAD Wasu da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da Maigarin Rijana, Alhaji Ayuba Dakolo Ayuba, a gonarsa da ke yankin Ƙaramar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna. Garin Rijana dai yana kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna, kuma yana kusa da tashar jirgin ƙasa, sannan ba shi da nisa da inda ’yan bindiga suka dasa wa fasinjojin da ke cikin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna bom kwanan baya.  Kamar yadda majiyar Blueprint Manhaja ta shaida, ta ce, an yi garkuwa da Maigari Ayuba ne da safiyar Alhamis lokacin da ya je duba gonarsa a…
Read More