Babban Labari

Zaɓen fidda gwani: APC ta ɗage zaɓen ‘yan takarar Shugaban Ƙasa, PDP ta shiga ruɗani

Zaɓen fidda gwani: APC ta ɗage zaɓen ‘yan takarar Shugaban Ƙasa, PDP ta shiga ruɗani

Daga BASHIR ISAH Jam’iyyar APC ta ɗage zaɓen fidda gwanin na ‘yan takarar Shugaban Ƙasa da ta shirya gudanarwa a ranar Litinin, 23 ga Mayun 2022, tare da cewa za ta sanar da sabon lokaci nan gaba. Duk da dai jam’iyyar ba ta ba da dalilin ɗage zaɓen ba, amma ba wannan ne karon farko da APC ta sauya jadawalin zaɓen fidda gwanin nata ba dangane da shirye-shiryen zaɓen 2023. Sanarwar da ta nuna ɗage zaɓen ta ce, “An ɗage shirin tantace ‘yan takarar Shugaban Ƙasa da aka shirya gudanarwa a ranar Litinin,  23 ga Mayun 2022. “Za a sanar…
Read More
Janar Yahaya: Sai da hannun farar hula tsaro zai dawo

Janar Yahaya: Sai da hannun farar hula tsaro zai dawo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A daidai lokacin da matsalar tsaron Nijeriya ta ƙi ci ta ƙi cinyewa, duk da ƙoƙarin da jami'an tsaron ƙasar ke cewa suna yi, Babban Hafsan Sojojin Ƙasan Nijeriya, Laftanar Janar Faruq Yahaya, jiya Alhamis a wajen wani taron ƙarawa juna sani, ya bayyana cewa dole ne jami'an tsaro su haɗa ƙarfi da ƙarfe da ƙungiyoyin fararen hula da sauran 'yan ƙasa a yaƙin da suke yi da 'yan ta'adda. Wakilinsa, Babban Hafsan Soji, Manjo-Janar Marcus Kangye, ya karanta saƙon Yahaya a wajen taron ƙara wa juna sani ga mahalarta kwas mai lamba 62022…
Read More
Yau Zamfara za ta karɓi baƙuncin Osinbajo

Yau Zamfara za ta karɓi baƙuncin Osinbajo

Daga SANUSI MUHAMMAD, a Gusau Gwamnatin jihar Zamfara da Jam’iyyar APC reshen jihar sun shirya tsaf domin tarbar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Yemi Osinbajo a wani ɓangare na rangadin da yake yi a jihohi. A yayin ziyarar tasa, ana sa ran Osinbajo zai gana da wakilan jihar da sarakuna 19 da ma Gwamnan Jihar, Bello Mohammed Matawalle. Jaridar Blueprint Manhaja ta ruwaito cewa, an baza jami’an tsaro daban-daban a sassan Gusau, babban birnin jihar domin tabbatar da ziyarar da Mataimakin Shugaban Ƙasar zai yi an kammala ta cikin kwanciyar hankali. Ana sa ran Osinbanjo ya isa Gusau da ƙarfe 2:30 na…
Read More
An ƙone matashiyar da ake zargi da ɓatanci ga Annabi a Sakkwato

An ƙone matashiyar da ake zargi da ɓatanci ga Annabi a Sakkwato

-A kai zuciya nesa, cewar Majalisar Sarkin Musulmi-Mun rufe kwalejin har illa masha Allahu – Gwamnati-’Yan sanda sun kama mutum biyu Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Matasa sun ƙone wata matashiya da ake zargi da yin ɓatanci ga Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammadu (SAW), a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sakkwato, lamarin da ya tilasta wa gwamnati rufe kwalejin ba tare da bayyana ranar da za a koma karatu ba. Ɗaruruwan ɗalibai da wasu mata sun gudanar da zanga-zanga tare da ciro wacce ake zargin daga maɓoyar da hukumomin makaranta suka ɓoye ta, inda suka kashe tare da ƙone…
Read More
Buhari ya roƙi ASUU ta janye yajin aikinta

Buhari ya roƙi ASUU ta janye yajin aikinta

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya miƙa roƙonsa ga Ƙungiyar Malaman Jami'o'i (ASUU) a kan ta janye yajin aikin da take yi sannan ta rungumi sulhu tsakaninta da Gwmanatin Tarayya. Haka nan, Buhari ya buƙaci ɗaliban da lamarin ya shafa su ƙara haƙuri da lamarin Gwamnatin Tarayya, kana ya hore su da kar su saka kansu cikin dukkan wani hali da ka iya zama barazana ga zaman lafiyar ƙasa. Buhari ya yi wannan roƙon da kiran ne a wajen taron karramawa na ƙasa da ya gudana a Babban Zauren Taro na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a…
Read More
Zaɓen 2023: Zan yi aiki tuƙuru wajen ƙarfafa nagartar Jihar Neja – Malagi

Zaɓen 2023: Zan yi aiki tuƙuru wajen ƙarfafa nagartar Jihar Neja – Malagi

Daga WAKILIN MU Ɗaya daga cikin manyan masu neman tsaya wa jam'iyyar APC takarar zama gwamna a Jihar Neja, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya sha alwashin zai fara aiki daga sa'ar farko da ya kama aiki a matsayin gwamna domin cimma burin sa na gina sabuwar nagartacciyar Jihar Neja idan har aka ba shi damar zama ɗan takarar jam'iyyar a zaɓen fidda gwani mai zuwa. Malagi, wanda shi ne Shugaban kamfanin buga jaridun Blueprint da Manhaja, ya faɗi haka ne a ranar Talata a lokacin da ya ke jawabi ga manema labarai jim kaɗan bayan ya miƙa fom ɗin sa…
Read More
Jonathan ya ziyarci shugaban jam’iyyar APC, ya nisanta kansa da ra’ayin takarar shugaban ƙasa

Jonathan ya ziyarci shugaban jam’iyyar APC, ya nisanta kansa da ra’ayin takarar shugaban ƙasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shirin naɗa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan a matsayin ɗan takarar jam’iyyar APC ya yi ƙaurin suna a ranar Litinin da ta gabata, inda sa'o'i kaɗan bayan faruwar hakan Jonathan ya ziyarci ofishin shugaban jam’iyyar, Abdullahi Adamu, domin nisanta kansa ga wannan mataki. An buga hotunan ziyarar ta yanar gizo a daren Litinin. Rahotanni sun ce Jonathan ya ziyarci Adamu a gidansa. An ɗauki hoton 'yan siyasar biyu suna tare da juna suna murmushi. Ziyarar na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan ƙungiyar 'Miyetti Allah Cattle Rearers', wata ƙungiyar Fulani ta sayi fom ɗin tsayawa takara da…
Read More
Jonathan ya yi watsi da fom ɗin da aka saya masa na takarar APC

Jonathan ya yi watsi da fom ɗin da aka saya masa na takarar APC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon shugaban ƙasar Nijeriya, Goodluck Jonathan ya nesanta kansa da fom ɗin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar APC da wata ƙungiya ta saya masa, inda ya yi watsi da batun tsayawa takara a babban zaɓen 2023. A wata sanarwa da ofishin yaɗa labaran tsohohon shugaban ƙasar ta fitar sa’o’i kaɗan bayan ƙungiyar ta sayi fom ɗin a kan Naira miliyan 100, Jonathan ya bayyana kyamarsa ga matakin, yana mai jaddada cewa shi ba ɗan jam’iyyar APC ba ne. “Saboda haka ana kira ga jama’a da su yi watsi da abin da ƙungiyar ta aikata, domin ba…
Read More
Shugaba Buhari ya tafi taron Majalisar Ɗinkin Duniya

Shugaba Buhari ya tafi taron Majalisar Ɗinkin Duniya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya keta hazo zuwa Abidjan a Ƙasar Cote d’Ivoire domin halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya. Taron zai maida hankali ne kan abin da ya shafi lalubo hanyoyin magance matsalolin zezayar ƙasa, fari, gushewar dazuzzuka da sauransu da kuma tasirinsu ga tattalin arzikin duniya. Wannan shi ne karo na goma sha biyar da MƊƊ ke shirya irin wannan taro wanda zai gudana daga ranar 9 zuwa 10 na watan Mayun 2022. Sanarwar da ta fito ta hannun Kakin Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu, ta nuna babban taron zai tattauna a kan matakan da suka…
Read More