Babban Labari

Martanin gwamnati ga Tinubu: ’Yan Nijeriya ne suka ɗora Buhari kan mulki ba kai ba

Martanin gwamnati ga Tinubu: ’Yan Nijeriya ne suka ɗora Buhari kan mulki ba kai ba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, miliyoyin ’yan Nijeriya ne suka zaɓi shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a zaɓen 2015. A cewar fadar shugaban ƙasa, babu wani mutum ɗaya da zai iya cewa shi ne ya ɗauki nauyin zaman Buhari shugaban ƙasa. Kalaman na zuwa ne a kan kalaman Bola Ahmed Tinubu, jigo a jam’iyyar APC na ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ranar Alhamis, 2 ga Yuni, 2022 a Abeokuta, jihar Ogun. Tinubu ya ce, “ba don ni ba, da Buhari bai tsaya ba, da bai zama shugaban ƙasa ba. Ya gwada a karo na…
Read More
Za mu ladabtar da Tinubu kan kalaman da ya zazzaga wa Buhari – Adamu

Za mu ladabtar da Tinubu kan kalaman da ya zazzaga wa Buhari – Adamu

Daga BASHIR ISAH Jam'iyyar APC ta ce za ta ladabtar da jagoranta na ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashinta, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, saboda kalaman da ya zazzaga wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kwanan nan. Shugaban APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai a babban ofishin jam'iyyar da ke Abuja a ranarAsabar da ta gabata. Idan za a iya tunawa, a kwanan nan aka ga wani bidiyon Tinubu na yawo yayin ziyarar neman ƙuri'un daliget da ya kai Jihar Ogun, inda a ciki bidiyon aka ji shi yana kalamai kan taimakon…
Read More
EFCC za ta ƙwace Jami’ar Nok da ke Kaduna

EFCC za ta ƙwace Jami’ar Nok da ke Kaduna

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata Kotu a Nijeriya ta umarci hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC ta ƙwace Jami'ar Nok mai zaman kanta mallaki wani tsohon babban jami'in gwamnati da ke fuskantar tuhuma kan rashawa. EFCC ta ce, Anthony Hassan, wanda tsohon darakta ne na harkokin kuɗaɗe a ma'aikatar lafiya, ya gina jami'ar ne da kuɗin rashawa. Sai dai wani abu da ba a fayyace ba, shi ne ko matakin zai shafi karatun ɗalibai a makarantar da ke Arewacin Kaduna. Kuma babu wasu ƙarin bayyanai kan ko Mista Hassan zai ɗaukaka ƙara. Sannan baya ga ƙwace jami'ar, akwai…
Read More
Rikicin APC: Sanata Abdullahi Adamu ya bada haƙuri

Rikicin APC: Sanata Abdullahi Adamu ya bada haƙuri

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya bada haƙuri a kan rikicin da ya kunno kai a kwanan nan. Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa kwanaki uku da su ka gabata ne dai wasu masu riqe da muƙamai a APC, Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Yamma, Malam Salihu Lukman da takwaransa na Kudu maso Yamma, Isaac Kekemeke su ka zargi Adamu da ajiye su a gefe a al’amuran jam’iyyar ba tare da yi da su ba. Sun zargi Adamu da yin abubuwa da dama waɗanda ba su dace ba…
Read More
Taron kasuwanci a Spaniya: Buhari na yi wa Nijeriya zawarcin zuba jari

Taron kasuwanci a Spaniya: Buhari na yi wa Nijeriya zawarcin zuba jari

• Ya ce Nijeriya ce mafi girman tattalin arziki a Afirka • Ya bada shawarar yadda ƙasashen Afirka da Turai za su fuskanci ƙalubalen yaƙin Rasha da Ukraine • A shirye muke mu tallafa wa 'yan kasuwar Spaniya - Minista Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙalubalanci masu zuba jari na ƙasar Spaniya da su yi amfani da yanayin da Nijeriya ke da shi na rashin biyan haraji da kuma kason ’yan ƙasashen waje marasa iyaka a yankunan cinikayya cikin ‘yanci na ƙasar domin haɓaka kasuwanci tsakanin Nijeriya da Spaniya da kuma bunƙasar tattalin arziki.…
Read More
Badaƙalar biliyan N200: Akanta Janar ya bayyana sunayen wasu a matsayin waɗanda ake zargi

Badaƙalar biliyan N200: Akanta Janar ya bayyana sunayen wasu a matsayin waɗanda ake zargi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Badaƙalar da ta shafi Akanta Janar na Tarayyar Nijeriya da aka dakatar, Ahmed Idris na iya cinye wasu jami’an gwamnati yayin da Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC) ta tsananta bincike. Rahotanni sun bayyana cewa, bisa sakamakon binciken da hukumar EFCC ta gudanar, jimillar kuɗaɗen da aka samu a cikin jerin badaƙalar hada-hadar kuɗaɗe da aka dakatar da Akanta Janar akansu ta kai Naira Biliyan 200 (N200,000,000,000). Idan za a iya tunawa cewa, jami’an EFCC sun kama Idris ne a ranar 16 ga Mayu, 2022 kan wasu zamba da aka fara tunanin Naira…
Read More
2023: Ku haɗa kanku don samar da nagartaccen shugabanci, kiran Buhari ga gwamnonin APC

2023: Ku haɗa kanku don samar da nagartaccen shugabanci, kiran Buhari ga gwamnonin APC

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yi kira ga gwamnonin APC da su zamo madu kiyaye ƙa'idojin jam'iyya yayin zaɓen fidda gwani na APC mai zuwa. Buhari ya yi wannan kira ne yayin wata ganawa da ya yi da gwamnonin na APC su 22 haɗe da Shugaban APC na Kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ranar Talata a fadar Villa da ke Abuja. Cikin wata sanarwa da ya fitar, mai magana da yawun Buhari, Femi Adesina, ya ce Shugaba Buharin ya ce, "Shirye-shiryen zaɓen 2023 sun kankama, kuma a sanina galibin nasarar jam'iyyun siyasa a sassan duniya ya danganta ne…
Read More
Zaɓen fidda gwani: Za mu kwatanta adalci a APC – Adamu

Zaɓen fidda gwani: Za mu kwatanta adalci a APC – Adamu

*Shugaban APC ya yi magana kan ɗan takarar masalaha da karɓa-karɓa*Dokar zaɓe na cigaba da kaɗa hantar gwamnoni*Yadda ta kaya a zaɓen fidda gwanin PDP a Borno da Yobe*Kada ku mayar da zaɓen fidda gwani na a-mutu-ko-a-yi-rai, inji Gwamna Masari Daga MAHDI M. MUHAMMAD A yayin da jam’iyyun Nijeriya za su ƙarƙare gudanar da zaven fitar da gwani na masu neman kujerar Shugaban Ƙasa a ƙarshen makon nan, Shugaban jam’iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce, jam’iyyar za ta yanke shawara kan batun shiyya-shiyya bayan ta tantance masu neman shugabancin ƙasar a 2023, ya na mai cewa, shugabannin…
Read More
Jirigin ƙasan Abuja-Kaduna: A gaggauta sako mana ’yan uwanmu, inji dangin waɗanda aka sace

Jirigin ƙasan Abuja-Kaduna: A gaggauta sako mana ’yan uwanmu, inji dangin waɗanda aka sace

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Iyalai da dangin waɗanda ’yan bindiga su ka sace a hanyar jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna sun bayyana damuwarsu akan irin halin da ’yan uwansu ke ciki a hannun masu garkuwar, inda suka ce a gaggauta a sako su. Sun bayyana hakan ne a cikin wata sanarwar da suka fitar cikin makon nan. Sanarwar ta ce, “a jiya, mun sami labari mai firgitarwa daga waɗanda suka sace fasinjojin jirgin Ak9 da suka taso daga Abuja ranar 28 ga Maris, 2022 da qarfe 6:10 na yamma zuwa Kaduna amma ba su kai ga inda aka nufa ba.”…
Read More