07
Jun
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, miliyoyin ’yan Nijeriya ne suka zaɓi shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a zaɓen 2015. A cewar fadar shugaban ƙasa, babu wani mutum ɗaya da zai iya cewa shi ne ya ɗauki nauyin zaman Buhari shugaban ƙasa. Kalaman na zuwa ne a kan kalaman Bola Ahmed Tinubu, jigo a jam’iyyar APC na ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ranar Alhamis, 2 ga Yuni, 2022 a Abeokuta, jihar Ogun. Tinubu ya ce, “ba don ni ba, da Buhari bai tsaya ba, da bai zama shugaban ƙasa ba. Ya gwada a karo na…
