Babban Labari

Gwamnati ta amince da batun buɗe sabbin jami’o’i 20 a faɗin ƙasa

Gwamnati ta amince da batun buɗe sabbin jami’o’i 20 a faɗin ƙasa

Daga AISHA ASAS Majalisar Zartarwa ta Tarayya, ta aminta da batun samar da sabbin jami'o'i masu zaman kansu guda 20 a faɗin ƙasa. Majalisar ta cim ma wannan matsaya ne yayin zamanta na Larabar da ta gabata ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu ya ce, jami'o'in za su samu lasisin zarafin gudanarwa ne daga hannun Hukumar Kula da Jami'o'i ta Ƙasa (NUC), wanda za su yi amfani da shi nan da shekaru uku masu zuwa, yayin da gwamnati za ta ci gaba da sanya musu ido. Jami'o'in da Majalisar ta amince da a kafa ɗin…
Read More
Rasuwar Momoh: Na rasa babban amini – inji Buhari

Rasuwar Momoh: Na rasa babban amini – inji Buhari

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa dangane da rasuwar amininsa Prince Tony Momoh. A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya fitar a Litinin da ta gabata a Abuja, Shugaba Buhari ya bayyana cewa, marigayin ya kasance tare da shi a duk faɗi-tashin da ya sha. Yana mai cewa, "Samun kwatankwacin marigayin wajen biyayya a fagen siyasa, abu ne mai wahalar gaske. Zan yi rashin sa matuƙa." Jaridar Manhaja ta kalato Buhari ya yi tuna baya inda ya ce, "Marigayi Momoh ya ba da gagarumar gudunmawa a matsayinsa na Shugaban Sashen Yaɗa…
Read More
Sadarwa: Gwamnati ta tsawaita wa’adin shirin haɗe layukan sadarwa da lambar NIN

Sadarwa: Gwamnati ta tsawaita wa’adin shirin haɗe layukan sadarwa da lambar NIN

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta ƙara wa'adin shirin haɗe Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa da layukan sadarwa da makonni 8 domin bai wa 'yan ƙasa isasshen lokaci don su sada layukan sadarwarsu da lambar NIN. Sabon wa'adin da gwamnatin ta tsayar yanzu, shi ne zuwa ranar 6 ga Afrilu mai zuwa. Daraktan Hulɗa da Jama'a na Hukumar Sadarwa ta Ƙasa, Dr Ikechukwu Adinde, shi ne ya ba da bayanin haka a ranar Talata. Inda ya ce, Ministan Sadarwa Isa Pantami ne ya ba da umarnin tsawaita wa'adin bayan taron kwamitin sanya ido kan shirin haɗe lambar NIN da layukana sadarwa.…
Read More
Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Ƙungiyar Kare 'Yancin Zamantakewa Da Yaƙi Da Cin Hanci (SERAP), ta yi kira ga Shugaban Majalisar Dattawa Dr Ahmad Lawan, da takwaransa na Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Femi Gbajabiamila, a kan su buƙaci hukumomin yaƙi da rashawa su binciki badaƙalar ɓatan dabon da kasafin biliyan N4.4 na Majalisar Tarayya ya yi kamar yadda rahotannin binciken ofishin Babban Jami'in Bincike na Ƙasa suka nuna. A wata wasiƙa da ta samu sa hannun mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ƙungiyar ta ce, "Ta hanyar kwatanta jagoranci nagari a kan wannan batu, Majalisar Tarayya za ta iya nuna wa 'yan Nijeriya cewa ɓangaren yin…
Read More
Yaƙi Da Matsalar Tsaro: Zulum ya ƙalubalanci shugabannin tsaro su kyautata alaƙa da takwarorinsu

Yaƙi Da Matsalar Tsaro: Zulum ya ƙalubalanci shugabannin tsaro su kyautata alaƙa da takwarorinsu

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Barno, Babagana Umara Zulum, ya ƙalubalanci sabbin shugabannin tsaro da su assasa kyakkyawar alaƙar aiki a tsakaninsu da ƙasashen da Nijeriya ke maƙwabtaka da su, wato Chadi da Kamaru da kuma Nijar. Kazalika, ya shawarci manyan hafsoshin da su kasance masu haƙuri da kuma sauraron jama'a a halin aiwatar da ayyukansu. Gwaman ya faɗa wa jami'an haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncinsu a fadar gwamnatin jihar a Lahadin da ta gabata yayin da suka yi ziyarar aiki ta farko a jihar. Shugaban tsaro Major-General Leo Irabor, shi ne ya jagoranci takwarorinsa Major-General Ibrahim Attahiru…
Read More
Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Daga FATUHU MUSTAPHA A ranar Asabar da ta gabata Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama cikakken dan jam'iyyarsu ta APC, a mahaifarsa Daura da ke jihar Katsina. Tare da kira ga daukacin shugabannin jam'iyyar da karfafa kwazo wajen tabbatar da APC ta samu karin tagomashi a matakin farko. Buhari ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karbi bakuncin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Lawan da wasu gwamnoni hada da wasu 'ya'yan jam'iyyar APC a garin Daura, jim kadan bayan ya kammala sabunta rijistarsa ta jam'iyya a Gundumar Sarkin Yara. A wata sanarwa da mai magana…
Read More
Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, rattaba hannu da ya yi a dokar Budaddiyar Jami'ar Nijeriya (NOUN) da aka yi wa gyaran fuska, ya haifar wa jami'ar da ɗalibanta samun tagomashi a kasa. Shugaban ya bayyana haka ne yayin bikin yaye daliban jami'ar karo na 9 da na 10 da aka hade wuri guda wanda ya gudana ta bidiyo a ranar Asabar da ta gabata. Da yake jawabi yayin bikin ta bakin wakilinsa Mataimakin Sakataren Hukumar Kula da Jami'o'i ta Kasa, Ramon Yusuf, Buhari ya ce, "Budaddiyar Jami'ar tana sauke nauyin da ya rataya a kanta…
Read More
Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Daga WAKILINMU Hukumar Birnin Tarayya, Abuja ta ce, za ta tabbatar da an bi dokokin yaki da Cutar Korona na 2021 kamar yadda Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da Cutar Korona ya shimfida. Hukumar ta bayyana haka ne a wajen wani taron masu fada a ji da ya gudana a karkashin jagorancin Ministan Abuja, Malam Muhammad Musa Bello, a Juma'ar da ta gabata a Abuja. Da yake jawabi yayin taron, Ministan Abuja ya ce, "Za a kara himma wajen wayar da kan mazauna Abuja game da kiyaye dokokin yaki da Cutar Korona, tare da tabbatar da an hukunta duk wanda…
Read More
Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Daga UMAR M. GOMBE Cibiyar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ta bayyana cewa, an samu rasuwar mutum 27 cikin sa'o'i 24 a fadin kasa sakamakon Cutar Korona. Cibiyar ta sanar da hakan ne a shafinta na intanet a Juma'ar da ta gabata, inda ta ce kawo yanzu adadin wadanda suka mutu a fadin kasa a dalilin korona ya cilla zuwa mutum 1,557. Kazalika, NCDC ta sanar an samu karin mutum 1,114 da suka harbu da cutar ta korona a fadin kasa. Wanda a cewarta, "Ya zuwa yanzu mutum 128,674 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a fadin kasa."…
Read More
Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Adaga FATUHU MUSTAPHA Fadar Shugaban Kasa ta sanar cewa sabbin shugabannin sojojin da aka nada kwanan nan za su bayyana gaban Majalisar Dattawa domin tabbatar da nadin nasu. A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a, Hadimin Shugaba Buhari Kan Harkokin Majalisar Tarayya (Bangaren Dattawa), Sanata Babajide Omoworare ya bayyana cewa, tuni Shugaba Buhari ya tura wasika ga Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, yana mai bukatar a tabbatar da nadin wadanda lamarin ya shafa. Sanarwar ta nuna cewa: “Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar da Majalisar Tarayya nadin da ya yi tare da neman majalisar ta tabbatar da nadin nasa…
Read More