Babban Labari

Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero: Sarkin da aka jima ana tsumayi…

Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero: Sarkin da aka jima ana tsumayi…

*Zai amshi sandar mulki gobe*Yadda aka shirya bikin ba shi sandar*Asali da tarihin bada sandar sarautar Daga BILKISU YUSUF ALI a Kano "SAI KA YI”Kalaman da suka yi fice a bakunan Kanawa kenan a lokacin da ya ke riƙe da sarautar hakimci. Fata nagari lamiri, ya tabbata ga Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, don a gobe Asabar, ranar 3 ga Yuli, 2021 ne Gwamnatin Jihar Kano ta ware da ƙawata ranar na yin mashahurin taron da aka jima ba a yi irinsa ba, don bayar da sanda, duba da tun gabanin taron Jihar Kano ta yi cikar…
Read More
Arahar fetur ta yi yawa a Nijeriya – NNPC

Arahar fetur ta yi yawa a Nijeriya – NNPC

*Ya kamata farashin fetur ya kai Naira 256 duk lita*Nijeriya na kashe Naira biliyan 150 duk wata kan tallafin mai – Mele Kyari*Nijeriya ba za ta iya jure biyan tallafin mai ba, inji shi Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Babban Manajan Darakta na kamfanin kula da mai na Nijeriya (NNPC), Malam Mele Kyari, ya bayyana cewa, bisa la’akari da irin kuɗin da Nijeriya ke kashewa wajen shigo da tataccen man fetur a ƙasar, za a iya cewa, farashinsa na Naira 162 a gwamnatance ya yi matuƙar kaɗan, yana mai cewa, aƙalla ya kamata a sayar da shi kan Naira…
Read More
Ba duk shugaba zai kasadar Zulum ba – Buhari

Ba duk shugaba zai kasadar Zulum ba – Buhari

*Shugaba Buhari ya gode wa ’yan Nijeriya da suke mara masa baya har yanzu Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, ba kowanne mai mulki ne zai iya yin irin kasadar da Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ke yi ba a cikin yanayi na matsalar tsaron da ke addabar jiharsa. Shugaba Buhari, wanda ya ke jawabi a lokacin da ya ziyarci Fadar Shehun Borno jiya a ziyarar aikin da ya kai jihar ta Borno, ya yaba wa Gwamna Zulum bisa yadda ya ke wucewa gaba ba dare ba rana kuma cikin rashin…
Read More
Masu garkuwa sun canja salo a Sakwkwato

Masu garkuwa sun canja salo a Sakwkwato

*Sun fara yin shigar burtu*Yanzu haka wani attajiri na hannunsu – Hon. Salihi*Ku ci gaba da ba mu muhimman bayanai – ’yan sanda Daga JAMIL GULMA a Sakkwato Masu garkuwa da mutane sun ɓullo da sabon salon ɗaukar mutane a waɗansu sassan Jihar Sakwkwato, inda yanzu suka ɓullo da sabon salon ɗaukar mutane ɗaya-bayan-ɗaya a gidajensu, maimakon kai farmaki a cikin babbar tawaga. Wakilin Manhaja mai kula jihohin Sakwkwato da Kebbi ya ziyarci waɗansu yankuna da suka haɗa da ƙananan hukumomin Illela, Gada da kuma Gwadabawa, inda abin ya fi ƙamari. Shugaban Ƙaramar Hukumar Illela, Hon. Injiniya Aliyu Salihu, ya…
Read More
Saɓa ƙa’ida: Tiwita ta goge saƙon Shugaba Buhari

Saɓa ƙa’ida: Tiwita ta goge saƙon Shugaba Buhari

Daga BASHIR ISAH Sakamakon abin da ya kira da saɓa wa dokokinsa, kamfanin Twitter ya share wani saƙon da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya wallafa a shafinsa na Twitter inda ya yi barazanar yin maganin waɗanda suka gagara ɗaukar izina daga yaƙin basasar da aka yi a Nijeriya. Rahotanni sun nuna da alama dai kamfanin ya goge saƙon Buharin ne bisa zargin saɓa dokokinsa. Cikin saƙon da ya wallafa a ranar Talata wanda bai yi wa Twitter daɗi ba, Buhari ya ce, "Galibin waɗanda ke nuna rashin ɗa'a ba su da masaniyar irin ɓanar da hasarar da aka tafka yayin…
Read More
Rasuwar Attahiru ta hana murnar kisan Shekau

Rasuwar Attahiru ta hana murnar kisan Shekau

*Har yanzu rundunar sojan Nijeriya na ci gaba da taka-tsantsan*Shin ko Nijeriya za ta amfana da nasarar ISWA kan Boko Haram?*Janar Yahaya: Wane ne wanda Buhari ya saka magajin Attahiru? Daga NASIR S. GWANGWAZO, a Abuja A ranar Alhamis, 27 ga Mayu, 2021, rahotanni suka fantsama a cikin Nijeriya da ƙasashen duniya cewa, ɗaya da daga cikin waɗanda Nijeriya da Amurka ke kallo a matsayin manyan maƙiyanta kuma jagoran ƙungiyar masu tayar da ƙayar baya da aka fi sani da Boko Haram, wato Abubakar Shekau, ya rasa ransa a wani artabu tsakanin mabiyansa da mambobin ɗaya ƙungiyar ita ma mai…
Read More
Dalilin da ya sa Buhari bai halarci jana’izar attahiru ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Dalilin da ya sa Buhari bai halarci jana’izar attahiru ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammad Buhari ya bayyana dalilin da ya sa bai samu halartar wurin jana'izar tsohon Shugaban Rundunar Sojoji, Lt. Gen. Ibrahim Attahiru tare da wasu jami'ai 10 da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata. Attahiru da sauran jami'ai goma sun cim ma ajali ne a haɗarin jirgin saman da ya rutsa da su a Juma'ar da ta gabata a Kaduna. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Shugaba Buhari na buƙatar bayanan tsaro na aƙalla sa'o'i 48 kafin ya ba fadarsa don halartar kowane irin taro. Da alama dai rashin ganin Buhari a wajen taron…
Read More