Babban Labari

Nijeriya ta karɓi rigakafin korona na farko, Buhari da mataimakinsa za su tsayar da ranar da za a yi musu rigakafin

Nijeriya ta karɓi rigakafin korona na farko, Buhari da mataimakinsa za su tsayar da ranar da za a yi musu rigakafin

Daga AISHA ASAS A balin da ake ciki, maganin rigakafin xutar korona na AstraZeneca ya iso Nijeriya. Wannan shi ne rigakafin korona na farko da Nijeriya ta samu wanda ake sa ran za a yi wa 'yan ƙasa bayan gwamnati ta kammala tsare-tsarenta gane da rigakafin. Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo, za su tsayar da ranar da kowannesu zai yi allurar rigakafin cutar korona a idon duniya ta hanyar amfani da rigakafin Oxford/AstraZeneca na rukunin farko guda milyan 4 da Nijeriya ta karɓa a wannan Talata. Darakta a Hukumar Bunƙasa Kula da Lafiya na Matakin Farko na…
Read More
Yadda aka kuɓutar da ɗaliban Jangeɓe da aka yi garkuwa da su

Yadda aka kuɓutar da ɗaliban Jangeɓe da aka yi garkuwa da su

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya bayyana cewa tubabbun 'yan fashi ne suka taimaka wa hukumomin tsaro wajen ceto ɗalibai mata na makarantar Jangeɓe da 'yan bindiga suka kwashe kwanan nan. Bayan kuɓutar da su ba tare da biyan wata diyya ba, Matawalle ya karɓi ɗaliban su 279 da asubahin Talata a birnin Gusau. A cewar Matawalle, "Wannan shi ne sakamakon shirinmu na ƙoƙarin dawo da zaman lafiya tare da kunyata waɗanda ke ra'ayin cewa babu tsaro a ƙasa. "Tun Juma'a muke tattaunawa da 'yan fashin inda muka cim ma yarjejeniya ranar Litinin da yamma har aka…
Read More
An sako ɗaliban Sakandaren Kagara

An sako ɗaliban Sakandaren Kagara

Daga FATUHU MUSTAPHA Bayanai daga Jihar Neja sun nuna an sako ɗalibai da malamai na Sakandaren Kimiyya Kagara da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su 'yan kwanakin da suka gabata. Wata majiya mai tushe ta tabbatar wa jaridar PRNigeria batun sakin ɗaliban a safiyar wannan Asabar. Idan dai za a iya tunawa, Manhaja ta ruwaito batun sace ɗaliban su 27 da ma'aikata 3 da iyalansu su 12, a ranar 17 ga Fabrairun 202.
Read More
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata kimanin 300 a Zamfara

‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata kimanin 300 a Zamfara

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotanni daga Jihar Zamfara, sun nuna cewa 'yan bindiga sun sace ɗalibai mata kusan su 300 a Makarantar Sakandaren Gwamnati (GSS) Jangeɓe, da ke yankin ƙaramar hukumar Talata-Mafara a jihar, a tsakar daren Juma'a. Kwamishinan Labarai na jihar, Malam Suleiman Tunau Anka, ya tabbatar wa manema labarai faruwar haka, inda ya ce 'yan bindiga sun shiga makatar ne da misalin ƙarfe 1 na tsakar daren Juma'a suka kwashi ɗalibai. Sai dai Anka bai faɗi adadin ɗaliban da lamarin ya shafa ba. Wannan na faruwa a daidai lokacin da Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle, ya yi kira ga…
Read More
Abuja: An yi jana’izar mayaƙan sama da suka rasu a haɗarin jirgin sama

Abuja: An yi jana’izar mayaƙan sama da suka rasu a haɗarin jirgin sama

Daga BASHIR ISAH An gudanar da jana'izar jami'an sojin saman nan su 7 da suka rasu a haɗarin jirgin sama da ya auku a Abuja a Lahadin da ta gabata. Jami'an da lamarin ya shafa sun cim ma ajalinsu ne bayan da jirginsu, ƙirar Beechcraft King Air 350, ya faɗo a ƙauyen Bassa daura da Babban Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe, bayan da suka tashi da nufin zuwa aiki a jihar Neja. Mai Magana da Yawun Rundunar Sojin Sama na Nijeriya, Air Vice Marshal Ibikunle Daramola ya ce jirgin ya fuskanci matsalar inji kafin aukuwar haɗarin. Cikin waɗanda suka…
Read More
Majalisa ta tabbatar da naɗin sabbin jakadu duk da ƙorafin da aka yi a kan su

Majalisa ta tabbatar da naɗin sabbin jakadu duk da ƙorafin da aka yi a kan su

Daga WAKILIN MU Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin tsoffin Shugabannin Tsaron Nijeriya a matsayin jakadu. Wanna ya faru ne a Talatar da ta gabata. Idan ba a manta ba, a Janairun da ya gabata Shugaba Buhari ya zaɓi General Abayomi G. Olonisakin da Lt. General Tukur Y. Buratai da Vice Admiral Ibok-Ete E. Ibas da kuma Air Marshal Sadique B. Abubakar don zama jakadun Nijeriya bayan murabus da suka yi daga aiki ba da jimawa ba. Amincewa da naɗin ya zo ne bayan gamsuwa da majalisar ta yi da rahoton kwamitin majalisar kan harkokin ƙasashen waje ƙarƙashin jagorancin Adamu…
Read More