22
May
21
May
Daga WAKILINMU Wani jirgin saman sojojin Nijeriya ɗauke da Shugaban Rudunar Sojoji, Ibrahim Attahiru tare da wasu jami''an rundunar,. ya yi haɗari. Duk da dai babu ciikakken bayani game da haɗari, amma dai bayanan da MANHAJA ta kalato sun nuna babu wanda ya tsira a haɗarin. A cewar majiyar MANHAJA, haɗarin ya auku ne da misalin ƙarfe 6 na yammacin Juma'a a babban filin jirgin saman Kaduna sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka samu. Rundunar Sojan Sama ta Nijeriya (NAF) ta tabbatar da aukuwar haɗarin. Sanarwar da rundunar ta fitar wadda ta samu sa hannun Daraktan Sashenta na Hulɗa…
21
May
*A baya jami’an tsaro ake zargin da kawo cikas*Yanzu ’yan daba sun hutasshe su*Shin ko bambancin salon mulkin APC da na PDP ne?*Yadda fusatattun matasa suka kai wa NLC hari a Kaduna Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja A Nijeriya lokutan gudanar da zanga-zangar nuna ƙin jinin gwamnati ko adawa da wani mataki da ta ɗauka an saba ganin yadda ta ke amfani da jami’an tsaro na ’yan sanda wajen tarwatsa masu zanga-zanga, inda ake zargin su da yin amfani da hayaƙi mai sa hawaye, motar ruwan zafi, kulake, wani lokacin ma har da harsashin bindiga ko makamatansu, don kawo…
18
May
Daga BASHIR ISAH Babban Lauyan Nijeriya kuma Ministan Shari'a, Abubakar Malami, ya tabbatar cewa Gwamnatin Tarayya ta karɓi maƙudan kuɗaɗe Fan milyan £4,214,017.66 na kuɗaɗen sata da aka danganta su da iyalan tsohon Gwamnan Jihar Delta, James Ibori. Mai taimaka wa ministan kan sha'anin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Umar Gwandu, shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja a ranar Talata. Bayanan Gwandu sun nuna an rigaya an saka kuɗaɗen a kwatankwacin Naira cikin asusun Gwamnantin Tarayya tun a 10 ga Mayu, 2021. Haka nan cewa Minista Malami ya rattaba hannu a takardar yarjejeniyar karɓar kuɗaɗen…
14
May
*Ɗahiru Bauchi ya ƙalubalanci Sarkin Musulmi*Tinubu ya nemi a yi wa Buhari addu’a*Saraki ya yi nasiha Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja A jiya Alihamis ne a Nijeriya da ma yawancin ƙasashen duniya aka gudanar da bikin ƙaramar Sallah ta bana, 13 ga Mayu, 2021 na shekarar Masihiyya, wacce ta zo daidai da 1 ga Shawwal, 1442 bayan Hijira, inda Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya buƙaci ’yan Nijeriya da su gudanar da addu’o’in maganta ayyukan ’yan ta’adda da kuma masu neman mulki ko ta halin ƙaƙa. Sallar idin kuma ta zo ne a daidai lokacin da fitaccen malamin addinin Islama…
11
May
Daga FATUHU MUSTAPHA Fadar Shugaban Ƙasa ta tabbatar da cewa ɓarayi sun yi yinƙurin shiga gidan Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ibrahim Gambari, da ke fadar shugaban ƙasa a Abuja da subahin Litinin da ta gabata. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu, ya ce wannan yinƙuri ne mara kan gado da ɓarayin suka yi wanda ba su kai ga cim ma manufarsu ba. A wani mai kama da wannan, Shehu ya ce a halin da ake ciki 'yan sanda sun bazama neman wani ɓarawo ruwa a jallo wanda shi ma ya yi yinƙurin shiga gidan Maikano Abdullahi…
10
May
Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta bayyana Laraba 12 da Alhamis 13 ga Mayu, 2021, a matsayin ranakun hutu na gama-gari domin bikin ƙaramar sallah na bana. Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, shi ne ya sanar da hakan a ranar Litinin a Abuja a madadin Gwamnantin Tarayya. Aregbesola ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga Musulmi 'yan Nijeriya na gida da ƙetare, da su yi amfani da wannan dama wajen yi wa Nijeriya addu'ar samun zaman lafiya mai ɗorewa da daidaiton tattalin arzikin ƙasa yayin bikin na Idul Fitr. Ministan ya ce babu yadda za a…
10
May
Daga UMAR M. GOMBE Shugaba Muhammadu Buhari ya kira ga 'yan Nijeriya da a kula tare da lura a lokacin bikin ƙaramar sallah na bana duba da cewa har yanzu annobar korona na ci gaba da yi wa duniya barazana. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu, ya ce a bisa dalilai na annobar korona ya sa a bana Shugaba Buhari tare da iyalansa da manyan jami’an gwamnatinsa za su gudanar da sallar Idi a cikin Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, suna masu kiyaye dokikin da aka shata din yaƙi da cutar korona. Sanarwar da Garba Shehu…
08
May
Daga UMAR M. GOMBE Rundunar 'yan sanda ta jihar Rivers ta tabbatar da mutuwar wasu jami'anta su bakwai sakamakon hare-haren da 'yan bindiga suka kai a jihar. Mai magana da yawun 'yan sandan jihar, SP Nnamdi Omoni, shi ne ya tabbatar da hakan A cewar jami'in, "Maharan sun kashe jami'ansu biyu a shingen binciken abubuwan hawa a ƙauyen Choba da ke tsakanin ƙaramar hukumar Obio/Akpor da ƙaramar hukumar Emohua, sannan suka banka wa wata mota mallakar ɗaya daga cikin jami'an da lamarin ya shafa." Kazalika, ya ce 'yan bindigar sun sake kai wa ofishin 'yan sanda hari a garin Rumuji…
07
May
Daga WAKILINMU Tsohuwar Ministar Harkokin Mata, Sanata Aisha Jummai Al-Hassan, wacce aka fi sani da suna Mama Taraba, ta rasu a wata asibitin ƙasar Masar, 7 ga Mayu, 2021. Wata majiya daga ahalin marigayiyar ce ta tabbatar wa Dateline Nigeria batun rasuwar. A halin rayuwarta, Jummai ta yi takarar kujerar gwamanan jihar Taraba a ƙarƙashin jam'iyyar APC a 2015. Ta riƙe muƙamin minista a gwamnatin Buhari. An haifi marigayiyar ce a Jalingo, a ranar 16 ga Satumban 1959.
