Babban Labari

Masu garkuwa sun canja salo a Sakwkwato

Masu garkuwa sun canja salo a Sakwkwato

*Sun fara yin shigar burtu*Yanzu haka wani attajiri na hannunsu – Hon. Salihi*Ku ci gaba da ba mu muhimman bayanai – ’yan sanda Daga JAMIL GULMA a Sakkwato Masu garkuwa da mutane sun ɓullo da sabon salon ɗaukar mutane a waɗansu sassan Jihar Sakwkwato, inda yanzu suka ɓullo da sabon salon ɗaukar mutane ɗaya-bayan-ɗaya a gidajensu, maimakon kai farmaki a cikin babbar tawaga. Wakilin Manhaja mai kula jihohin Sakwkwato da Kebbi ya ziyarci waɗansu yankuna da suka haɗa da ƙananan hukumomin Illela, Gada da kuma Gwadabawa, inda abin ya fi ƙamari. Shugaban Ƙaramar Hukumar Illela, Hon. Injiniya Aliyu Salihu, ya…
Read More
Saɓa ƙa’ida: Tiwita ta goge saƙon Shugaba Buhari

Saɓa ƙa’ida: Tiwita ta goge saƙon Shugaba Buhari

Daga BASHIR ISAH Sakamakon abin da ya kira da saɓa wa dokokinsa, kamfanin Twitter ya share wani saƙon da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya wallafa a shafinsa na Twitter inda ya yi barazanar yin maganin waɗanda suka gagara ɗaukar izina daga yaƙin basasar da aka yi a Nijeriya. Rahotanni sun nuna da alama dai kamfanin ya goge saƙon Buharin ne bisa zargin saɓa dokokinsa. Cikin saƙon da ya wallafa a ranar Talata wanda bai yi wa Twitter daɗi ba, Buhari ya ce, "Galibin waɗanda ke nuna rashin ɗa'a ba su da masaniyar irin ɓanar da hasarar da aka tafka yayin…
Read More
Rasuwar Attahiru ta hana murnar kisan Shekau

Rasuwar Attahiru ta hana murnar kisan Shekau

*Har yanzu rundunar sojan Nijeriya na ci gaba da taka-tsantsan*Shin ko Nijeriya za ta amfana da nasarar ISWA kan Boko Haram?*Janar Yahaya: Wane ne wanda Buhari ya saka magajin Attahiru? Daga NASIR S. GWANGWAZO, a Abuja A ranar Alhamis, 27 ga Mayu, 2021, rahotanni suka fantsama a cikin Nijeriya da ƙasashen duniya cewa, ɗaya da daga cikin waɗanda Nijeriya da Amurka ke kallo a matsayin manyan maƙiyanta kuma jagoran ƙungiyar masu tayar da ƙayar baya da aka fi sani da Boko Haram, wato Abubakar Shekau, ya rasa ransa a wani artabu tsakanin mabiyansa da mambobin ɗaya ƙungiyar ita ma mai…
Read More
Dalilin da ya sa Buhari bai halarci jana’izar attahiru ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Dalilin da ya sa Buhari bai halarci jana’izar attahiru ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammad Buhari ya bayyana dalilin da ya sa bai samu halartar wurin jana'izar tsohon Shugaban Rundunar Sojoji, Lt. Gen. Ibrahim Attahiru tare da wasu jami'ai 10 da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata. Attahiru da sauran jami'ai goma sun cim ma ajali ne a haɗarin jirgin saman da ya rutsa da su a Juma'ar da ta gabata a Kaduna. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Shugaba Buhari na buƙatar bayanan tsaro na aƙalla sa'o'i 48 kafin ya ba fadarsa don halartar kowane irin taro. Da alama dai rashin ganin Buhari a wajen taron…
Read More
Shugaban Rundunar Sojoji, Ibrahim Attahiru ya rasu a haɗarin jirgin sama a Kaduna

Shugaban Rundunar Sojoji, Ibrahim Attahiru ya rasu a haɗarin jirgin sama a Kaduna

Daga WAKILINMU Wani jirgin saman sojojin Nijeriya ɗauke da Shugaban Rudunar Sojoji, Ibrahim Attahiru tare da wasu jami''an rundunar,. ya yi haɗari. Duk da dai babu ciikakken bayani game da haɗari, amma dai bayanan da MANHAJA ta kalato sun nuna babu wanda ya tsira a haɗarin. A cewar majiyar MANHAJA, haɗarin ya auku ne da misalin ƙarfe 6 na yammacin Juma'a a babban filin jirgin saman Kaduna sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka samu. Rundunar Sojan Sama ta Nijeriya (NAF) ta tabbatar da aukuwar haɗarin. Sanarwar da rundunar ta fitar wadda ta samu sa hannun Daraktan Sashenta na Hulɗa…
Read More
Tarwatsa zanga-zanga: ’Yan daba sun maye gurbin ’yan sanda

Tarwatsa zanga-zanga: ’Yan daba sun maye gurbin ’yan sanda

*A baya jami’an tsaro ake zargin da kawo cikas*Yanzu ’yan daba sun hutasshe su*Shin ko bambancin salon mulkin APC da na PDP ne?*Yadda fusatattun matasa suka kai wa NLC hari a Kaduna Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja A Nijeriya lokutan gudanar da zanga-zangar nuna ƙin jinin gwamnati ko adawa da wani mataki da ta ɗauka an saba ganin yadda ta ke amfani da jami’an tsaro na ’yan sanda wajen tarwatsa masu zanga-zanga, inda ake zargin su da yin amfani da hayaƙi mai sa hawaye, motar ruwan zafi, kulake, wani lokacin ma har da harsashin bindiga ko makamatansu, don kawo…
Read More