27
Oct
•Kotun ta yi fatali da shaidar takardun Chicago•Ta raraki Peter Obi•Tinubu ye nemi haɗin kai don gina Nijeriya•Atiku da Obi su jira zuwa 2031, cewar Ganduje•PDP da LP sun maida martani•Buhari ya yi maraba da hukuncin Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun Ƙolin Nijeriya ta tabbatar da nasarar Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasar na 2023. Hukuncin na alƙalai bakwai ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Inyang Okoro ya ce, “a ƙarshe, bayan warware duk wasu lamurra game da ɗaukaka ƙarar, zan iya cewa babu hujjoji masu ƙwari game da ɗaukaka ƙarar, saboda haka an yi watsi…