Babban Labari

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu

Daga BASHIR ISAH A ranar Laraba Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya rataɓɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu ta 2024. Da wannan, sabuwar dokar za ta fara aiki ke nan, inda za ta bai wa ɗalibai a manyan makarantu zarafin samun rance daga gwamnati domin gudanar da harkokin karatunsu. Tinubu ya sanya wa dokar hannu ne bayan da Majalisar Tarayya ta nazarci rahoton Kwamitin Kula da Manyan Makarantu da kuma asusun TETFund.
Read More
Kisan Okuama: Mun ci alwashin adalci ga sojojin da aka kashe – DHQ

Kisan Okuama: Mun ci alwashin adalci ga sojojin da aka kashe – DHQ

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hedikwatar Tsaron Nijeriya ta ci alwashin cewa, ba za ta gajiya ba har sai an kama waxanda suka kashe sojoji 17 a Okuama da ke jihar Delta tare da gurfanar da su a gaban shari’a bisa ga dokar Nijeriya. Daraktan yaɗa labarai na tsaro, Manjo Janar Edward Buba ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa manema labarai qarin haske kan ayyukan soji da ke gudana a sassan ƙasar nan a Abuja, babban birnin Nijeriya. Janar Buba ya ce "an saki sunayen mutane takwas da ake nema ruwa a jallo ciki har…
Read More
Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Daga BASHIR ISAH Bayabnan da Manhaja ta tattaron sun ce, a jimilIance wasu sabbin gwamnoni su 13 sun ci bashi da ya kai Naira Biliyan 226.8 a cikin watanni shida da suka yi a ofis. Wannan bashin kuwa ya shafi wanda gwamnonin suka ci a gida da kuma ƙetare. Binciken News Point Nigeria ya gano cewa, wasu gwamnonin jihohi 16 kuma, basussukan da suka ciyo ya ƙaruwa da Naira Biliyan 509.3. An yi lissafin basussukan ƙetaren ne kan lissafin N889 kan $1 kamar yadda Ofishin Kula da Basussuka (DMO) ya nuna. Rahoton DMO ya ce an tattaro bayanan basussukan ne…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tinubu ta ware N90bn don cikata wa maniyyata kuɗin Hajji

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tinubu ta ware N90bn don cikata wa maniyyata kuɗin Hajji

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ta ware Naira biliyan 90 domin cikata wa maniyyata kuɗin Hajjin Bana. Tallafin na zuwa ne biyo bayan ƙarin kuɗin Hajji da aka yi bayan sama da Naira miliyan huɗu da maniyyatan suka yi da farko. A farkon wannan makon ne Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ba da sanarwar cewa, an yi ƙarin kuɗin Hajjin bana da Naira Miliyan 1.9 wanda kuma ake buƙatar kowane maniyyaci ya biya a cikin ƙankanin lokaci ko kuma ya haƙura da tafiya Hajji bana. Tun bayan sanarwar ƙarin da NAHCON ta yi,…
Read More
Sojoji sun ga bayan Dogo Gide

Sojoji sun ga bayan Dogo Gide

Daga BASHIR ISAH Rahotanni sun ce dakarun ƙasar Nijar sun ga bayan gawurtaccen ɗan bindigar nan, Dogo Gide, na mayaƙan ANSARU da sauran ƙungiyoyin 'yan ta'adda. MANHAJA ta kalato cewar, Dogo Gide ya mutu ne sakamakon raunin da ya ji biyo bayan musayar wutar da aka yi tsakanin rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadarin Daji (OPHD) a dajin Madada da yankin Ƙaramar Hukumar Maru a ranar 12 ga Maris, 2024. An ce duk da raunin da aka yi injuries, Dogo Gide, sai da aka san yadda aka yi aka saci jiki aka shigar da shi asibiti a yankin Mabera a…
Read More
Yanzu-Yanzu: Kotu ta yanke wa ɗan China hukuncin kisa kan kisan Ummita a Kano

Yanzu-Yanzu: Kotu ta yanke wa ɗan China hukuncin kisa kan kisan Ummita a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Babbar Kotun Jihar Kano, ta yanke wa ɗan Chinan nan, Frank Geng Quarong hukuncin kisa ta hanyar rataya. Mai Shari’a Sunusi Ado Ma’aji ne ya yanke masa hukuncin, bayan tabbatar da hujjojin da masu gabatar da ƙara suka yi a gaban kotun. Idan za a iya tunawa Manhaja ta rawaito tun a ranar 16 ga watan Satumba 2022, Frank Geng, ya hallaka Ummita a unguwar Janbulo da ke jihar Kano.
Read More
Ɗaliban Kuriga sun shaƙi iskar ‘yanci

Ɗaliban Kuriga sun shaƙi iskar ‘yanci

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga Jihar Kaduna na nuni da cewa, ɗaliban firamaren da aka yi garkuwa da su kwanan baya a yankin Kuriga a jihar, sun shaƙi iskar 'yanci. Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, shi ne ya ba da sanarwar hakan a shafinsa na Facebook ranar Asabar da tsakar dare Idan za a iya tunawa, MANHAJA ta rawaito a ranar 8 ga Maris wasu 'yan bindiga suka kai hari yankin Kuriga, cikin Ƙaramar Hukumar Chilun a jihar Kaduna, inda suka yi awon gaba da yara sama da 200. Sai dai Gwamnan bai yi wani cikakken bayani kan sako yaran…
Read More
Hedikwatar Tsaro na neman su Dogo Gide, Simon Ekpa, Bello Turji da sauransu ruwa a jallo

Hedikwatar Tsaro na neman su Dogo Gide, Simon Ekpa, Bello Turji da sauransu ruwa a jallo

Daga BASHIR ISAH A ƙalla 'yan bindiga, ɓarayin daji da tsageru 97 ne Babban Ofishin Tsaro da ke Abuja ya bayyana a matsayin waɗanda yake nema ruwa a jallo. Ofishin ya ce waɗanda yake neman suna da hannu wajen aikata manyan laifuka da tada zaune tsaye a sassan ƙasa. Har wa yau, waɗanda lamarin ya shafa ya haɗa da shugaban wani ɓangare na tsagerun IPOB, wato Simon Ekpa. Mai magana da yawun rundunar soji, Manjo-Janar Edward Buba, shi ne ya bayyana sunaye da hotun waɗanda rundunar ke farautarsu. MANHAJA ta rawaito a makon jiya cewa, Babban Ofishin tsaro na shirin…
Read More
An sace fasinjoji a hanyar Ƙanƙara dake Katsina 

An sace fasinjoji a hanyar Ƙanƙara dake Katsina 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wasu ’yan bindiga sun yi sace fasinjoji da dama a wani harin da suka kai a Ƙaramar Hukumar Ƙanƙara da ke Jihar Katsina. Lamarin ya faru ne a jiya Alhamis bayan da ’yan bindigar dajin suka tare wata mota ƙirar bas mai cin mutane 18 mai lamba 14B-300-KT cike maƙil da fasinjoji mallakar hukumar kula da sufuri ta Jihar Katsina (KSTA). Wani ganau ya shaida wa majiyarmu ta wayar tarho cewa, galibin fasinjojin da ke cikin motar sun fito ne daga Ƙaramar Hukumar Funtuwa a kan hanyarsu ta zuwa Katsina, Babban Birnin Jihar Katsina.…
Read More
‘Yan binga sun sace mutum 61 a wani sabon hari a Kaduna

‘Yan binga sun sace mutum 61 a wani sabon hari a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga jihar Kaduna sun ce aƙalla mutum 61 wasu da ake zargin 'yan fashin daji ne suka yi garkuwa da su a yankin Buda da ke cikin Ƙaramar Hukumar Kajuru a jihar. Duk da dai babu bayani a hukumance ka aukuwar harin, sai dai wani mazaunin yankin ya shaida wa majiyarmu ranar Talata cewar, maharan sun dira ƙauyen ne da misalin ƙarfe 11:45 na dare inda suka yi awon gaba da mutum 61. A cewar Dauda Kajuru wanda mazaunin yankin ne, 'yan bindigar shiga yankin da yawansu, kuma sun harba bindiga. Ta bakinsa, “abin da ya…
Read More