Babban Labari

Shari’ar zaɓen 2023: Yadda Tinubu ya yi zarra a Kotun Ƙoli

Shari’ar zaɓen 2023: Yadda Tinubu ya yi zarra a Kotun Ƙoli

•Kotun ta yi fatali da shaidar takardun Chicago•Ta raraki Peter Obi•Tinubu ye nemi haɗin kai don gina Nijeriya•Atiku da Obi su jira zuwa 2031, cewar Ganduje•PDP da LP sun maida martani•Buhari ya yi maraba da hukuncin Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun Ƙolin Nijeriya ta tabbatar da nasarar Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasar na 2023. Hukuncin na alƙalai bakwai ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Inyang Okoro ya ce, “a ƙarshe, bayan warware duk wasu lamurra game da ɗaukaka ƙarar, zan iya cewa babu hujjoji masu ƙwari game da ɗaukaka ƙarar, saboda haka an yi watsi…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta yi watsi da buƙatar Atiku ta neman gabatar da sabuwar hujja a kan Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta yi watsi da buƙatar Atiku ta neman gabatar da sabuwar hujja a kan Tinubu

Daga BASHIR ISAH Kotun Ƙoli ta yi watsi da buƙatar da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugabancin ƙasa na Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya gabatar wa kotun ta neman kotu ta ba shi damar gabatar mata da sabuwar hujja a kan Shugaban Ƙasa Bola Tinubu. Atiku ya buƙaci kotun da ta ba shi damar gabatar da bayanan da ya ce ya samo game da karatun da Tinubu ya ce ya yi a Jami'ar Jihar Chicago ta ƙasar Amurka. Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar na ra'ayin cewa bayanan bogi ne Tinubu ya miƙa wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a…
Read More
Zamfara: Dauda ya ƙara yi wa Matawalle fallasa

Zamfara: Dauda ya ƙara yi wa Matawalle fallasa

*Gwamna ya zargi ministan da wawure biliyoyin kuɗi na aikin filin jirgi*Za a gurfanar da masu hannu ciki a gaban kuliya Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga dukkan alamu zazzafar adawar siyasar dake tsakanin Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, da wanda ya gaje shi kuma Ƙaramin Ministan Tsaro, Muhammad Bello Matawalle, na ƙara yin tsamari a tsakaninsu, inda a baya-bayan nan gwamnan ya zargi ministan da wawure biliyoyin Dala na aikin gina filin jiragen sama na jihar ta Zamfara. Lawal ya ce, gwamnatin da ta shuɗe ta Bello Matawalle ta wawure biliyoyin Naira a filin jirgin sama na Zamfara, wanda daga…
Read More
Ana zargin almundahana a rabon kayan tallafin Kebbi 

Ana zargin almundahana a rabon kayan tallafin Kebbi 

*An dakatar da rabon tallafin Argungu Daga JAMIL GULMA a Kebbi  A ranar Juma'ar da ta gabata ne Gwamnan Jihar Kebbi, Malam Nasir Idris wanda shine Ƙauran Gwandu, ya ƙaddamar da rabon kayan tallafi a Ƙaramar Hukumar Maiyama, don rage raɗaɗin matsin tattalin arziki ga al'ummar jihar, inda kuma daga nan ya umarci kowacce ƙaramar hukumar mulki ta je ta raba a yankinta. Sai dai ba a nan gizo ke saƙa ba, saboda rabon kayan ya samu tarnaƙi yayin da a ke zargin tafka almundahana a waɗansu ƙananan hukumomi. Wata mata da ba ta so a bayyana sunanta ba ta…
Read More
Chicago: Zan dangana idan Kotun Ƙoli ta tsarkake Tinubu – Atiku

Chicago: Zan dangana idan Kotun Ƙoli ta tsarkake Tinubu – Atiku

*Ɗan takarar PDP ya ce ba don kansa yake wa Tinubu tone-tone ba*Siyasarka ta zo ƙarshe – APC ga Atiku*Ba na tsoro domin Buhari ya gama kassara kasuwancina a Nijeriya, inji Atiku Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Ɗan takarar babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya kuma tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya yi iƙirarin cewa, idan har Kotun Ƙolin Nijeriya ta yanke hukuncin cewa, Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu tsarkakke ne shi, duk da satifiket ɗin da shi Atikun ya amso daga Jami’ar Chicago dake Birnin Ilinious, don ƙalubalantar sahihancin zaɓensa a 2023, to zai dangana ya haƙura…
Read More
Ranar Samun ‘Yancin Kan Ƙasa: Tinubu ya yi wa ma’aikata ƙarin albashi na wucin-gadi

Ranar Samun ‘Yancin Kan Ƙasa: Tinubu ya yi wa ma’aikata ƙarin albashi na wucin-gadi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana ƙarin albashi ga ma'aikatan gwamnati don rage musu raɗaɗin cire tallafin mai. Ya sanar da hakan ne a jawabinsa da ya yi wa 'yan ƙasa da safiyar Lahadi albarkacin Ranar Samun 'Yancin Kan Ƙasa, 1 ga Oktoba, 2023. Game da ƙarin, Tinubu ya ce ƙaramin ma'aikaci zai samu ƙarin N25,000 a albashinsa har na tsawon wata shida. Wannan na nufin ma'aikacin gwamnatin tarayya da ke karɓar albashi N30,000, yanzu N55,000 zai riƙa karɓa har na tsawon wata shida. Da alama dai ƙarin albashin na wucin gadi ne, kuma Shugaban bai yi ƙarin haske…
Read More
Ruɗani ya mamaye hukuncin kotun zaɓen Gwamnan Kaduna

Ruɗani ya mamaye hukuncin kotun zaɓen Gwamnan Kaduna

*Shugaban Kotun ya kori ƙarar*Alqalai biyu sun nemi yin tutsu?*Gwamna Sani ya yaba wa Ashiru Kudan*PDP ta kasa gamsuwa Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga dukkan alamu hukuncin da kotun sauraron ƙarar zaɓen kujerar Gwamnan Jihar Kaduna ta yanke ya jefa mutane da dama cikin ruɗani, inda da fari aka bayar da rahotannin da ke nuni da cewa, kotun ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba (wato inconclusive), to amma jim kaɗan bayan hakan sai kuma sababbin rahotanni suka nuna cewa, hukuncin yana magana ne akan tabbatar da Gwamna Uba Sani na Jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe…
Read More
Yau Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi

Yau Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi

Yau Lahadi ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai yi wa 'yan ƙasa jawabi bayan dawowa daga taron da ya halarta a Amurka. Taron shi ne karo na 78 da Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya wanda ya gudana a birnin New York. Bayan kammala taron ne Shugaba Tinubu ya ziyarci Paris da Faransa don taƙaitaccen hutu, in ji wata majiya. Tinubu ya iso gida ne sa'o'i kafin Ranar Samun 'Yancin Kan Nijeriya karo na 63, sannan kawana huɗu gabanin tsunduma yajin aikin da Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya da takwarorinta suka shirya. Da misalin ƙarfe 7:00am na wannan safiya…
Read More
An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

Jama'a sun shiga halin ruɗani game da shari'ar zaɓen gwamna a jihar Kaduna. Hakan ya faru ne bayan da wani rahoto ya nuna Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe na Gwamnan Jihar ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba. Bayan kimanin awa guda da fitan rahoton, sai aka sake ganin wani rahoto na daban na cewa, kotun ta tabbatar da nasarar da Gwamna Uba Sani ya samu a zaɓen wanda hakan ke nuni da shi ne zaɓaɓɓen gwamnan jihar. Da yake yi wa Jaridar News Point Nigeria ƙarin haske game da hukuncin ta waya, lauyan Gwamna Sani, Ibrahim H O…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Kaduna, ta ayyana zaɓen gwamnan jihar da ya gudana ran 18 ga Maris a matsayin wanda bai kammala ba, wato 'inconclusive.' Kotun ta ayyana hakan ne a zaman yanke hukunci kan shari'ar da ta yi a ranar Alhamis. Kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Victor Oviawe ta bai wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, da ta gudanar da zaɓen cike giɓi a cikin kwana 90. Da wannan hukuncin, ana sa ran INEC ta sake shirya zaɓe a gundumomi bakwai a tsakanin ƙananan hukumomi huɗu kuma a rumfunan zaɓe 24 masu ɗauke da masu kaɗa ƙuri'a…
Read More