01
May
Daga MAHD MUSA MUHAMMAD A ci gaba da shari’ar zargin juyin mulkin kan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya a gaban Babban Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, wani jami’in soja ya bayyana yadda masu bincike suka bankaɗo ainihin zargin shirin juyin mulki da nufin kifar da gwamnatin Tinubu tare da bayyana alaƙar raba kuɗi da tsare-tsaren da ake zargin masu hannu a ciki da su. Shaidan, wanda ya ce yana aiki da ɓanngaren rundunar ’yan sandan soji, wato Nigerian Army Corps of Military Police (NACMP), ya bayar da shaida ne a shari’ar wani tsohon manjo janar da…
