Babban Labari

Hausawan Jos ’yan ƙasa ne, inji kotu

Hausawan Jos ’yan ƙasa ne, inji kotu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babbar Kotun Jihar Filato mai lamba ta 17 ta yanke hukuncin cewa, duk wani Bahaushe da aka haifa kuma ya taso a ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa yana da cikakken haƙƙin a ɗauke shi a matsayin ɗan asalin yankin. Alƙali C. Donglong ne ya yanke hukuncin yayin da yake yanke hukunci a ƙarar da Fatima Baba Akawu da Baba Alhaji Akawu suka shigar a gaban kotun kan ƙin ba Fatima takardar shaidar asali (Certificate of Indigene) daga ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa. Masu ƙarar sun nemi kotun ta tantance ko Fatima Baba Akawu, wadda aka haifa…
Read More
Faɗan daba ya zama ‘gida-gida’ a Kano

Faɗan daba ya zama ‘gida-gida’ a Kano

Yadda al'amura suka dagule a unguwar Nasarawa Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A baya-bayan nan, ayyuykan daba sun sun mamaye lungu da saƙo na birnin Kano, Babban Birnin Jihar Kano, inda aka fara jin al’ummar jihar, musamman malamai, suna hawa munbari suna kiraye-kiraye kan batun. A baya an fi samun rikicin a unguwannin talakawan birin kamar ɗorayi, Rijiyar Lemo, Birged, Fagge, ƙofar Nasarawa da dai makamantansu sun yi ƙaurin suna wajen guje-guje, saboda yadda ’yan daba kan faɗa wa mutane babu gaira babu dalili baya ga kashe mutane ta hanyar ƙwacen waya da ya yi ƙaurin suna. Bugu da ƙari, al’ummar…
Read More
Zaɓen fidda gwanin ADC: Magoya bayan El-Rufai na zargin an yaudare su

Zaɓen fidda gwanin ADC: Magoya bayan El-Rufai na zargin an yaudare su

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Rikicin cikin gida na ci gaba da ƙamari a jam’iyyar ADC reshen Jihar Kaduna, yayin da wasu daga cikin magoya bayan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, ke zargin sa da yin watsi da tsarin siyasar da ya tsaya masa tsayin daka tsawon shekaru. Abin da ya fara a matsayin saɓani kan zaɓen fidda gwani na kujerar gwamna da na ’yan majalisa yanzu ya rikiɗe zuwa babbar ɓaraka a cikin jam’iyyar, inda masu biyayya ga El-Rufai ke zargin cewa an yi watsi da biyayyarsu da sadaukarwar da suka yi ta hanyar yarjejeniyoyin sirri da kuma amfani da…
Read More
Zaɓukan APC: Wasu sun dara, wasu sun koka

Zaɓukan APC: Wasu sun dara, wasu sun koka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Zaɓukan fidda gwani na Jam’iyyar ‘All Progressiɓes Congress’ (APC) da aka gudanar a sassa daban-daban na Niijeriya sun bar baya da ƙura, rikice-rikice, koke-koke, zarge-zargen maguɗi da murnar nasara daga ɓangarori mabambanta, yayin da jam’iyyar ke ƙoƙarin tsara dabarun tunkarar babban zaɓen shekarar 2027. Yayin da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar suka samu tikitin takara cikin farin ciki da gagarumar nasara, wasu kuwa sun bayyana zaɓukan a matsayin “wasan kwaikwayo” da aka shirya domin fifita wasu ‘yan takara, lamarin da ya haddasa zanga-zanga da kuma barazanar ɗaukaka ƙorafe-ƙorafe zuwa matakin ƙasa. A wasu jihohi, an…
Read More
ACI: Rikicin ACF abin kunya ne ga Arewa

ACI: Rikicin ACF abin kunya ne ga Arewa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Kungiyar haɗin kan arewacin Nijeriya da zaman lafiya da bunƙasa, wato Arewa Cohesion for Peace, Unity and Development Initiative (ACI) ta nuna rashin jin daɗinta kan rikicin shugabanci da ke addabar ƙungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), tana mai bayyana lamarin a matsayin abin kunya da ya jefa Arewacin Nijeriya cikin ba’a da raini a idon jama’a. A cikin wata sanarwa da Darakta Janar na ƙungiyar, Dr. Abdullahi Idris, ya aikewa da manema labarai, ACI ta bayyana damuwarta kan yadda rikice-rikice, zarge-zarge da rarrabuwar kai suka yi ƙamari a cikin ACF. Kungiyar ta ce rikicin…
Read More
ACF ta afka rikici kan biliyoyin Naira

ACF ta afka rikici kan biliyoyin Naira

*An dakatar da Shugaban Kwamitin Amintattu Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kwamitin Zartarwa na ƙasa na ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ya dakatar da Shugaban Kwamitin Amintattu na ƙungiyar, Alhaji Bashir M. Dalhatu, bisa zargin almundahanar kuɗi da take ƙa’idojin kundin tsarin mulki, a wani mataki mai tsauri da ya ƙara ruruta rikicin shugabanci a cikin ƙungiyar. An yanke wannan hukunci ne a wani taron gaggawa na NEC da aka gudanar a Kaduna a ranar Laraba, a daidai lokacin da ake taƙaddama kan rahotannin hana shiga hedikwatar ACF da ‘yan sanda suka yi gabanin tarurrukan da aka shirya gudanarwa. Yayin da…
Read More
Yadda aka tsara kifar da gwamnatin Tinubu

Yadda aka tsara kifar da gwamnatin Tinubu

Daga MAHD MUSA MUHAMMAD A ci gaba da shari’ar zargin juyin mulkin kan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya a gaban Babban Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, wani jami’in soja ya bayyana yadda masu bincike suka bankaɗo ainihin zargin shirin juyin mulki da nufin kifar da gwamnatin Tinubu tare da bayyana alaƙar raba kuɗi da tsare-tsaren da ake zargin masu hannu a ciki da su. Shaidan, wanda ya ce yana aiki da ɓanngaren rundunar ’yan sandan soji, wato Nigerian Army Corps of Military Police (NACMP), ya bayar da shaida ne a shari’ar wani tsohon manjo janar da…
Read More
2027: Yadda hukuncin kotu zai rikita ADC da PDP

2027: Yadda hukuncin kotu zai rikita ADC da PDP

*Ana cikin zaman ɗar-ɗar bayan da Kotun ƙoli ta jinkirta yanke hukunta Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A wani sabon salo na rikice-rikicen dambarwar siyasa da suke ƙara dagula harkokin jam’iyyun adawa a Nijeriya, Kotun ƙoli ta Nijeriya ta jingine yanke hukunci kan shari’un da suka shafi rikicin shugabanci a cikin jam’iyyun ADC da kuma PDP, lamarin da ya haifar da damuwa da zaman ɗar-ɗar kan yiwuwar shigar su babban zaɓen 2027. Kwamitin alƙalai biyar ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Lawal Garba ne ya sanar da cewa, za a fitar da ranar yanke hukunci bayan kammala gabatar da hujjoji daga ɓangarorin…
Read More
Gaskiyar lamarin harin Jilli – Ministan Tsaro

Gaskiyar lamarin harin Jilli – Ministan Tsaro

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Ministan Tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya fito ya kare harin sama da sojoji suka kai a yankin Jilli da ke Jihar Borno, yana mai jaddada cewa waɗanda aka kashe ba fararen hula ba ne, illa mutanen da ke taimaka wa ’yan ta’adda da kayayyaki da tallafi. Ministan tsaron bya bayyana haka ne yayin wata hira da ya yi a tashar Arise, bayan wani babban taron tsaro da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta. Ya ce, harin ya samo asali ne daga sahihan bayanan sirri, inda aka kai farmaki kan wani wuri da…
Read More
Harin Boko Haram ya halaka janar a Borno

Harin Boko Haram ya halaka janar a Borno

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wasu da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram/ISWAP ne sun kai wani mummunan hari da tsakar dare a garin Benisheikh da ke ƙaramar Hukumar Kaga a Jihar Borno, inda suka hallaka wani babban jami’in rundunar soji, Birgediya Janar O. O. Braimah. Rahotanni sun bayyana cewa marigayin ya kasance kwamandan rundunar haɗin gwiwa a yankin, kuma ya rasu ne yayin da yake jagorantar dakarunsa a fafatawar da suka yi da maharan. Majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1 na dare ranar Alhamis, a wani salo na hare-hare da aka…
Read More