Babban Labari

Yadda aka tsara kifar da gwamnatin Tinubu

Yadda aka tsara kifar da gwamnatin Tinubu

Daga MAHD MUSA MUHAMMAD A ci gaba da shari’ar zargin juyin mulkin kan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya a gaban Babban Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, wani jami’in soja ya bayyana yadda masu bincike suka bankaɗo ainihin zargin shirin juyin mulki da nufin kifar da gwamnatin Tinubu tare da bayyana alaƙar raba kuɗi da tsare-tsaren da ake zargin masu hannu a ciki da su. Shaidan, wanda ya ce yana aiki da ɓanngaren rundunar ’yan sandan soji, wato Nigerian Army Corps of Military Police (NACMP), ya bayar da shaida ne a shari’ar wani tsohon manjo janar da…
Read More
2027: Yadda hukuncin kotu zai rikita ADC da PDP

2027: Yadda hukuncin kotu zai rikita ADC da PDP

*Ana cikin zaman ɗar-ɗar bayan da Kotun ƙoli ta jinkirta yanke hukunta Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A wani sabon salo na rikice-rikicen dambarwar siyasa da suke ƙara dagula harkokin jam’iyyun adawa a Nijeriya, Kotun ƙoli ta Nijeriya ta jingine yanke hukunci kan shari’un da suka shafi rikicin shugabanci a cikin jam’iyyun ADC da kuma PDP, lamarin da ya haifar da damuwa da zaman ɗar-ɗar kan yiwuwar shigar su babban zaɓen 2027. Kwamitin alƙalai biyar ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Lawal Garba ne ya sanar da cewa, za a fitar da ranar yanke hukunci bayan kammala gabatar da hujjoji daga ɓangarorin…
Read More
Gaskiyar lamarin harin Jilli – Ministan Tsaro

Gaskiyar lamarin harin Jilli – Ministan Tsaro

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Ministan Tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya fito ya kare harin sama da sojoji suka kai a yankin Jilli da ke Jihar Borno, yana mai jaddada cewa waɗanda aka kashe ba fararen hula ba ne, illa mutanen da ke taimaka wa ’yan ta’adda da kayayyaki da tallafi. Ministan tsaron bya bayyana haka ne yayin wata hira da ya yi a tashar Arise, bayan wani babban taron tsaro da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta. Ya ce, harin ya samo asali ne daga sahihan bayanan sirri, inda aka kai farmaki kan wani wuri da…
Read More
Harin Boko Haram ya halaka janar a Borno

Harin Boko Haram ya halaka janar a Borno

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wasu da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram/ISWAP ne sun kai wani mummunan hari da tsakar dare a garin Benisheikh da ke ƙaramar Hukumar Kaga a Jihar Borno, inda suka hallaka wani babban jami’in rundunar soji, Birgediya Janar O. O. Braimah. Rahotanni sun bayyana cewa marigayin ya kasance kwamandan rundunar haɗin gwiwa a yankin, kuma ya rasu ne yayin da yake jagorantar dakarunsa a fafatawar da suka yi da maharan. Majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1 na dare ranar Alhamis, a wani salo na hare-hare da aka…
Read More
Yadda sabon rikicin Jos ya dawo ɗanye

Yadda sabon rikicin Jos ya dawo ɗanye

*IGP Disu ya ziyarci Filato  *'Yan majalisun tarayya daga Filato sun kai ziyarar jaje Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU, a Jos  Al'ummar garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato, sun sake shiga wani sabon ruɗani da firgici sakamakon ɓarkewar wani sabon rikici, wanda ya samo asali daga harin ’yan bindiga da aka kai wani yanki na unguwar Rukuba da ake kira Gari Ya Waye, inda ake cin kasuwar dare da mashaya. An kai wannan hari ne ranar Lahadi, 29 ga Maris, 2026, da daddare da misalin ƙarfe 8:00 na dare, yayin da yankin ke tsaka da hada-hada, kamar yadda aka saba. Wannan…
Read More
A wane hali Sheikh Khalifa Zaria ke ciki?

A wane hali Sheikh Khalifa Zaria ke ciki?

*Jita-jitar rasuwarsa a hannun hukuma ta fara yawa *An kama shi bisa zargin hannu a juyin mulki Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Ana ci gaba da nuna damuwa a Nijeriya game da raɗe-raɗin rasuwar malamin addinin Musulunci a ƙasar, Sheikh Sani Abdulkadir Khalifa Zaria da ke tsare a hannun Hukumar Tsaron Farin Kaya ta (DSS). Tun bayan ɓullar wani bidiyo a shafukan sada zumunta da wani matashi ya yi iƙirarin rasuwar malamin, hankula suka tashi a sassan ƙasar musamman daga iyalai da ɗalibansa. Masu rajin kare haƙƙin ɗan'adam da manyan 'yansiyasa a ƙasar na ci gaba da yin tambayoyin…
Read More
Nijeriya ba ƙashin yarwa ba ce, inji Sarki Charles

Nijeriya ba ƙashin yarwa ba ce, inji Sarki Charles

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Ziyarar aiki ta tarihi da Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya kai ƙasar Birtaniya ta kai ƙololuwa a ranar Laraba, yayin da shi da Sarkin Birtaniya, King Charles III, suka gabatar da muhimman jawabai a wata babbar liyafar gwamnati da aka shirya a Fadar Windsor da ke Ingila, inda sarkin ya bayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ba ƙashin yarwa ba. Rahotanni sun nuna cewa taron, wanda ya samu halartar manyan ‘yan gidan sarauta ciki har da Sarauniya Camilla da Yarima William tare da Catherine, Yariman Wales, ya sake jaddada dangantaka mai ƙarfi da tarihi tsakanin…
Read More
Kisan Ayatollah: Ba makawa sai mun ɗauki fansa – Iran

Kisan Ayatollah: Ba makawa sai mun ɗauki fansa – Iran

*An yi mana kisan ƙare dangi, inji Mojtaba Khamenei *Amurka ta kashe Dala biliyan 11 a kwana shida na yaƙin Iran Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, ya ce, Iran za ta ɗauki fansar mutanenta da aka kashe, ciki har da yara da ɗaliban makarantar Minab, baya ga jagoran addini, Ayatollah Khamenei da aka kashe a farkon yaƙinta da Amurka da kuma Isra’ila. Ya bayyana hakan ne a sanarwarsa ta farko da ya fitar tun bayan da aka naɗa shi a matsayin sabon jagoran addinin ƙasar wanda gidan talabijin gwamnatin ƙasar ta karanto. "Dole…
Read More
Yaƙin Iran ya zama barazana ga duniya

Yaƙin Iran ya zama barazana ga duniya

*Tattalin arziki da zaman lafiya na fuskantar rashin tabbas *Cikakken rahoto kan yaƙin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rikicin da ya ɓarke tsakanin ƙasashen Iran da Isra’ila tare da shigar ƙasar Amurka ya ƙara dagulewa bayan kashe jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei a wasu hare-haren da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar. Bayan harin, Shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci al'ummar Iran su tuntsurar da gwamnatin ƙasar. Rikicin dai ya zama ɗaya daga cikin manyan batutuwan tsaro da siyasa da ke ɗaukar hankalin duniya a halin yanzu. Rahotanni daga manyan kafafen…
Read More
Yadda SSS ta saki Walida bayan shekara uku

Yadda SSS ta saki Walida bayan shekara uku

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Bayan kusan shekaru uku na ruɗani, zarge-zarge da muhawara mai zafi a faɗin ƙasa, Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (SSS) ta miƙa Walida Abdulhadi Ibrahim ga gwamnatin jihar Jigawa. A daren Laraba ne gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi, ya karɓi Walida a hedikwatar DSS da ke Abuja da misalin ƙarfe 10:40 na dare, bayan makonni na matsin lamba daga ƙungiyoyin farar hula da kuma sa ido daga jama’a. Da yake jawabi bayan karɓar, Gwamna Namadi ya bayyana Walida a matsayin “’yar jihar Jigawa,” yana mai ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar da tsaron…
Read More