ukarofi

11000 Posts
Yadda mata ke sayar da ƙwon haihuwarsu domin sayen abinci a Nijeriya

Yadda mata ke sayar da ƙwon haihuwarsu domin sayen abinci a Nijeriya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A faɗin Nijeriya, ana samun ƙaruwar yadda matasa mata ke sayar da ƙwayayen haihuwarsu, domin samun kuɗaɗen biyan buƙatun rayuwa, lamarin da ke haifar da muhawara kan illolinsa ga lafiya da kuma tarbiyya. Binciken da Weekend Trust ta gudanar ya nuna cewa cibiyoyin kula da matsalolin haihuwa sun zama wuraren da ɗalibai mata da sauran matasa ke zuwa domin sayar da ƙwayayen haihuwarsu. Wasu sun ce sun yi hakan ne domin biyan kuɗin makaranta, wasu kuma domin sayen gashin doki, tufafi da wayoyin hannu, yayin da wasu uwayen da ke renon yara su kaɗai suka ce…
Read More
Wacce wainar aka toya a taron ’yan midiya na Arewa?

Wacce wainar aka toya a taron ’yan midiya na Arewa?

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ba da jimawa ba ne aka gudanar da wani taron matasa ’yan Arewa masu rubuce-rubuce a zaurukan sada zumunta, a wani yunƙuri na haɗa kan matasan maza da mata, ƙarfafa musu gwiwa, da kuma samar musu da wata alƙibla ta yadda rubuce-rubucen da suke yi za su riƙa samar musu da natija mai kyau. Ofishin babban mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin watsa labarai da wayar da kai, Abdul'Aziz Abdul'Aziz ne ya shirya wannan taro, wanda aka gudanar a babban ɗakin taro na fadar gwamnatin Kano, a ranar Litinin 6 ga watan Yuli, 2026.…
Read More
Daular Shehu da Shehu kafin Allah ne

Daular Shehu da Shehu kafin Allah ne

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Marigayi Dokta Musa ɗankwairo Maradun ya ce Shehu 3 ag ga Nijeriya Shehu Sakkwato da Shehun Borno sai marigayi Shehu Usman Abubakar na Gombe. A nan kan Shehu na farko da na biyu na ke magana ko ma dai kai tsaye Daular Sokoto da Daular Borno. Wadannan biyun dauloli biyu ne da a ka yi a yankin Arewa da kewaye kuma na addinin musulunci. Duk da zuwan Turawa ya sauya tarihinsu amma har gobe tasirinsu na nan daram. Ba abun da ya ƙarfafa tasirin sai bin tsarin addinin Musulunci wajen ibada da kyautatawa kowa da Musulmi…
Read More
An gudanar da taron zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a Augie

An gudanar da taron zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a Augie

Daga JAMIL GULMA a Kebbi An gudanar da wani muhimmin taron zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a ƙaramar hukumar Augie da ke jihar Kebbi, domin ƙarfafa zaman lafiya da warware matsalolin da suka shafi rikice-rikicen noma da kiwo a yankin. Taron ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da manoma suka gabatar, inda suka zargi wasu makiyaya da yin ɓarna ga amfanin gonakinsu da ke tudu da kuma fadamomi. Da yake jawabi a wajen taron da aka gudanar a sakatariyar ƙaramar hukumar Augie, Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) reshen Augie, Alhaji Shehu Rugga, ya yi alƙawarin ci…
Read More
Buhari ya bar Nijeriya cikin kyakkyawan yanayi – Hadi Sirika

Buhari ya bar Nijeriya cikin kyakkyawan yanayi – Hadi Sirika

Daga UMAR GARBA a Katsina Tsohon ministan sufurin jiragen sama, Sanata Hadi Sirika, ya bayyana cewa marigayi tsohon Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya bar Nijeriya cikin yanayi na ci gaba, tare da ingantaccen tattalin arziki da tsaro mai kyau. Da yake magana a tashar ARISE TV, Sirika ya ce gwamnatin Buhari ta gaji matsaloli masu yawa, amma ta samu nasarori wajen yaƙi da Boko Haram, inda ta ƙwato ƙananan hukumomi 17 da 'yan ta'adda suka mamaye tare da ceto wasu daga cikin ɗaliban Chibok da aka sace. Ya kuma ce inganta tsaro ya bai wa al'umma damar komawa noma, zuwa…
Read More
2027: KMT ne mafita ga Yobe – Hajiya Amina Amana

2027: KMT ne mafita ga Yobe – Hajiya Amina Amana

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Fitacciyar 'yar siyasa a Jihar Yobe, Hajiya Amina Amana, ta bayyana cewa Barrista Kashim Musa Tumsa (KMT) shi ne mutumin da ya fi dacewa ya jagoranci Jihar Yobe a matsayin gwamna a shekarar 2027, tana mai cewa al'ummar jihar za su amfana matuƙa idan aka ba shi dama. Hajiya Amina ta bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ta yi da wakilinmu a lokacin da ta kai ziyara Jihar Gombe. A cewarta, duk da cewa Barrista Kashim Musa Tumsa bai taɓa riƙe wani babban muƙamin siyasa ba, ya yi wa al'ummar Yobe ayyukan alheri…
Read More
Kotu ta bada belin Dr Bishir Kurfi don sauraron shari’a 13 ga Yuli

Kotu ta bada belin Dr Bishir Kurfi don sauraron shari’a 13 ga Yuli

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Kotun majistare a Katsina ta bada belin Dr Bishir Kurfi zuwa 13 ga watan Yuli ranar da za ta cigaba da sauraran ƙarar da gwamnatin Jihar Katsina ta shigar tana zargin sa da ƙarya da ɓata su. A wata hira da gidan talabijin na Trust TV Dr Kurfi ya yi zargin cewa gwamnatin Jihar Katsina ta ɗauki nauyin 'yan bindiga zuwa aikin hajji wanda gwamnatin ta ƙaryata ta kuma buƙaci Dr Kurfi ya janye ƙazafin da ya yi. Lauyan wanda ake ƙara Barista AD umar ya bayyana wa manema labarai bayan da aka fito daga…
Read More
Kogon Katsina, Hakimin Sabuwa a Jihar Katsina ya rasu

Kogon Katsina, Hakimin Sabuwa a Jihar Katsina ya rasu

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Allah ya yi wa Hakimin Sabuwa kuma Kogon Katsina Injiniya Bello Ibrahim Kogo rasuwa. Wata majiyar ta nuna cewa marigayi Bello Kogo ya rasu a wata asibiti da ke Kano bayan ya yi fama da rashi lafiya. Babu wani ƙarin bayani sai ana sa ran gobe Talata za ayi jana'izar hakimin a gidan sa da ke garin Sabuwa a ƙaramar hukumar Sabuwa.
Read More
Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya cika shekara ɗaya da rasuwa

Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya cika shekara ɗaya da rasuwa

Daga UMAR GARBA a Katsina A yau 13 ga Yulin 2026 tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Muhammadu Buhari, ke cika shekara ɗaya da rasuwa, Buhari ya rasu a ranar 13 ga Yulin 2025 bayan ya shafe shekaru yana jagorantar ƙasar a matsayin shugaban mulkin soja da kuma shugaban ƙasa na farar hula. Buhari ya fara shugabancin Najeriya a matsayin shugaban mulkin soja daga shekarar 1983 zuwa 1985, kafin daga bisani ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2015, inda ya sake samun wa'adi na biyu a 2019. Ya miƙa mulki ga magajinsa bayan kammala wa’adinsa a shekarar 2023. Blueprint Manhaja ta…
Read More
Bilkisu Yusuf: Matar da ta rusa katangar da ke hana mata jagorantar ɗakunan labarai

Bilkisu Yusuf: Matar da ta rusa katangar da ke hana mata jagorantar ɗakunan labarai

"Ba ta rubutu don faranta wa masu mulki, kuma ba ta rubutu don ta jawo cece-kuce" A tarihin Nijeriya, akwai wasu mata da ba a auna darajarsu da mukaman da suka riƙa ko lambobin yabo da suka tara. Ana ci gaba da tuna su ne saboda irin sauyin da suka kawo a rayuwar al'umma da kuma kyawawan abubuwan da suka bari a baya. Shafin Gimbiya na wannan makon ya zaƙulo ɗaya daga cikin irin waɗannan fitattun mata, wato Bilkisu Yusuf; mace mai hangen nesa, ƙwararriyar 'yar jarida, gogaggiyar edita kuma fitacciyar mai fafutukar tabbatar da adalci da ci gaban al'umma.…
Read More