ukarofi

11474 Posts
Nijeriya ta kashe tiriliyan N3.14 wajen biyan bashin cikin gida a zangon farko na 2026 – DMO

Nijeriya ta kashe tiriliyan N3.14 wajen biyan bashin cikin gida a zangon farko na 2026 – DMO

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ofishin Kula da Basussukan ƙasa (DMO) ta ce Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira tiriliyan 3.14 wajen biyan bashin da ta biyo na cikin gida a zangon farko na shekarar 2026. Jaridar Tribune ta rawaito cewa wannan na ƙunshe a cikin rahoton da DMO ta fitar kan basukan da ake bin gwamnatin Nijeriya a cikin gida, inda ya baiyana cewa cikin kudin, an kashe Naira tiriliyan 2.97 wajen biyan kudin ruwa na bashin, yayin da aka biya Naira biliyan 169.68 a matsayin wani bangare na gundarin bashin. A watan Janairu, gwamnati ta kashe Naira biliyan…
Read More
Yadda na samu rancen biliyan N2.5 domin zuba jari a harkar noma — Buni

Yadda na samu rancen biliyan N2.5 domin zuba jari a harkar noma — Buni

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya bayyana yadda ya samu rancen Naira biliyan 2.5 daga Bankin Noma na ƙasa (BoA) da Bankin Masana’antu (BoI) jim kaɗan bayan hawansa mulki a shekarar 2019, domin zuba jari a harkar noma da bunƙasa tattalin arzikin jihar. Buni ya ce ya samu Naira biliyan biyu daga Bankin Masana’antu, yayin da ya samu ƙarin Naira miliyan 500 ta wani shirin shiga tsakani na Babban Bankin Nijeriya (CBN), wanda Bankin Noma ya jagoranta. Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a Gidan Gwamnatin Jihar Yobe da…
Read More
’Yan bindiga sun kai hari Alƙaleri, sun jikkata mutane, sun kwashe shanu

’Yan bindiga sun kai hari Alƙaleri, sun jikkata mutane, sun kwashe shanu

Daga MUAZU HARDAWA a Bauchi Mazauna yankin Fego da Ruga Maikasuwa da ke ƙasar Gwana a ƙaramar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi, sun nemi taimakon gwamnatin jihar da hukumomin tsaro bayan ’yan bindiga sun kai musu hari a tsakiyar daren Asabar zuwa wayewar Lahadi. Sheikh Yusuf Bello Gafaka, wani malami daga ƙasar Gwana, ya shaida wa wakilinmu a Bauchi cewa ’yan bindigar sun sake kai hari yankin ne kamar yadda suka yi a watannin baya, lamarin da ya tilasta wa wasu mazauna yankin yin hijira zuwa Jihar Gombe da wasu garuruwa domin tsira da rayukansu. Ya ce bayan ɗaukar tsauraran…
Read More
Kaunar ƙasa ce ta sa na shirya juyin mulki kan Tinubu – Kanar Ma’aji

Kaunar ƙasa ce ta sa na shirya juyin mulki kan Tinubu – Kanar Ma’aji

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kanar Mohammed Ma’aji na Rundunar Sojin Nijeriya, wanda ake zargi da jagorantar wani shirin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta hanyar juyin mulki, ya bayyana cewa abin da ya sa aka shirya shirin ba wata buƙata ta neman mulki ba ce, sai dai abin da ya kira kishin ƙasa da damuwa kan tabarbarewar tsaro da tattalin arzikin ƙasar. An gano shirin ne a watan Satumba na 2025 kafin a aiwatar da shi, lamarin da ya haifar da kama da binciken jami’an soja masu ci da waɗanda suka yi ritaya, da kuma wasu…
Read More
Daliba ta rasu bayan faɗowa daga bene mai hawa huɗu

Daliba ta rasu bayan faɗowa daga bene mai hawa huɗu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata ɗalibar Makarantar Koyon Aikin Shari’a ta Nijeriya mai shekara 23, Faith Alayande, ta rasu bayan ta faɗo daga saman ginin ɗakunan kwanan ɗalibai mai hawa huɗu a harabar makarantar da ke yankin Victoria Island a Jihar Legas. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Legas ta tabbatar cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Juma’a, 7 ga Agusta 2026. Kakakin rundunar, Abimbola Adebisi, ta ce mai kula da ɗakunan kwanan ɗaliban ce ta sanar da ’yan sanda bayan an gano ɗalibar ba ta cikin hayyacinta a harabar makarantar. A cewar Adebisi, wata ɗaliba da wani…
Read More
Yadda uwargidan Adeleke ta jagoranci zanga-zangar mata akan rikice-rikice a Jihar Osun

Yadda uwargidan Adeleke ta jagoranci zanga-zangar mata akan rikice-rikice a Jihar Osun

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Uwargidan Gwamnan Jihar Osun, Titilola Adeleke, ta jagoranci zanga-zangar mata a jihar domin nuna adawa da abin da suka bayyana a matsayin kame-kame ba tare da ka’ida ba da kuma tashin hankula, gabanin zaben gwamnan jihar da za a gudanar ranar Asabar. Matan, wadanda suka fito daga kungiyoyin ’yan kasuwa da masu sana’o’i daban-daban, sun yi tattaki daga hanyar Osogbo zuwa Ilobu, inda suka nufi hedikwatar rundunar ’yansandan jihar da ke Osogbo. Adeleke ta bukaci ’yansanda su gudanar da bincike kan wasu jiga-jigan jam’iyyar APC da take zargi da hannu wajen tashin hankulan da…
Read More
Tsaron ƙasa ya fara ne da kula da jin daɗin ‘yan ƙasa  — Sarki Sanusi

Tsaron ƙasa ya fara ne da kula da jin daɗin ‘yan ƙasa  — Sarki Sanusi

Daga RABIU SANUSI a Kano Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, CON, ya bayyana cewa tsaron kowace ƙasa yana farawa ne daga kare rayuka, walwala da jin daɗin al’ummarta, yana mai jaddada cewa tsaro bai tsaya kawai kan kare iyakokin ƙasa ba. Sarkin ya bayyana hakan ne a lokacin da yake matsayin uban taron wata gagarumar ƙungiyar ƙa’idar Dokokin Jinƙai ta Duniya da Kwalejin Shari’a ta Jami’ar Northwest Kano suka shirya, inda ya gabatar da babban jawabi mai taken “Jagoranci, Zaman Lafiya da Rawar da Cibiyoyin Gargajiya ke Takawa wajen gina ƙasa.” Mai Martaba ya bayyana cewa bai…
Read More
Adeleke ya zargi Oyetola da matsa wa EFCC ta rufe asusun Jihar Osun

Adeleke ya zargi Oyetola da matsa wa EFCC ta rufe asusun Jihar Osun

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya zargi tsohon gwamnan jihar, Gboyega Oyetola, da kasancewa a bayan matakin da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta ɗauka na daskarar da asusun gwamnatin jihar. Adeleke ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin wani taron Arise Town Hall da aka shirya domin ’yan takarar kujerar gwamnan Jihar Osun, gabanin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar 15 ga Agusta. Gwamnan ya yi zargin cewa Oyetola, wanda a yanzu yake riƙe da muƙamin Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arziƙin Teku, yana amfani da sunan…
Read More
Ƙungiyar kamfen ɗin Mahadi Aliyu za su tafi kotu bisa cire sunan ɗan takarar gwamnan ADC a Zamfara

Ƙungiyar kamfen ɗin Mahadi Aliyu za su tafi kotu bisa cire sunan ɗan takarar gwamnan ADC a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Kungiyar yaƙin neman zaɓen Mahdi Aliyu Gusau ta ƙi amincewa da ɗora sunan Bilyaminu Shinkafi a shafin yanar gizon hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, a matsayin ɗan takarar gwamna na Jam'iyyar African Democratic Congress, ADC, a Jihar Zamfara. Ƙungiyar ta bayyana hakan a matsayin wata dabarar da ba ta dace ba kuma ta yi alƙawarin ƙalubalantar sa a kotu. A cikin wata sanarwa da ta fitar a Gusau ranar Juma'a, wadda ƙungiyar yaƙin neman zaɓen ta sanya wa hannu, ta dage cewa Mahdi Gusau shine halartaccen ɗan takarar gwamna na ADC a…
Read More
Kwamishina ya yabi malaman tsangaya kan goyon bayan Inuwa da Jamilu gwamna a 2027

Kwamishina ya yabi malaman tsangaya kan goyon bayan Inuwa da Jamilu gwamna a 2027

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Kwamishinan ƙananan hukumomi na Jihar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya yaba wa malaman tsangaya na jihar bisa goyon bayan da suka bayyana wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya da ɗan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar APC, Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a zaɓen 2027. Kwamishinan ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala wani babban taro da ƙungiyar malaman tsangaya ta jihar ta gudanar, inda malaman suka bayyana aniyarsu ta mara wa Dakta Jamilu Gwamna baya tare da tabbatar masa da ƙuri’u 150,000 a zaɓen 2027. Ya ce matakin malaman na…
Read More