ukarofi

11670 Posts
Sarkin Rano ya naɗa sabon Chiroma tare da ɗaga darajar wasu dagatai biyu

Sarkin Rano ya naɗa sabon Chiroma tare da ɗaga darajar wasu dagatai biyu

Daga SULEIMAN HUSSAINI D/KUDU a Kano A Kano, Mai Martaba Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Umar Isa (Autan Bawo), ya naɗa ɗansa a matsayin Chiroman Rano, kuma Hakimin Gundumar Gwamma, tare da ɗaga darajar wasu Dagatai biyu zuwa Hakimai Masu Gunduma. An gudanar da bikin naɗin ne a fadar Sarkin da ke garin Rano ranar Juma’ar da ta gabata. Bikin naɗin ya samu halartar Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf; Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Hon. Abdurrahman Suleiman Kawu Sumaila; ɗan Majalisa mai wakiltar ƙananan hukumomin Rano, Bunkure da Kibiya, Rt. Hon. Kabiru Alasan Rurum; wakilan sarakunan Kano, Karaye…
Read More
Ku fi mayar da hankali kan buƙatun al’umma — Barista Ahmad

Ku fi mayar da hankali kan buƙatun al’umma — Barista Ahmad

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Kwamishinan ƙananan hukumomi da cigaban al’umma na Jihar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya buƙaci sabbin shugabannin ƙananan hukumomi 11 da na yankunan cigaban ƙananan hukumomi (LCDA) 13 da su mayar da hankali kan muhimman buƙatun al’ummominsu domin samar da ci gaba mai ma’ana a yankunansu. Kwamishinan ya yi wannan kiran ne a Bauchi a lokacin da yake yi wa shugabannin ƙananan hukumomin ƙarin haske kan ayyukan ci gaba da gwamnatin jihar ke aiwatarwa. Ya ce ya kamata kowane shugaban ƙaramar hukuma ya fahimci abubuwan da al’ummarsa suka fi buƙata, sannan ya gabatar da su…
Read More
Duwan ya zama shugaban kwamitin shirin KT1T na shiyyar Daura

Duwan ya zama shugaban kwamitin shirin KT1T na shiyyar Daura

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, Ph.D., ya amince da naɗin Hon. Shafi’u Abdu Duwan a matsayin shugaban kwamitin shirin Katsina One-Person-One-Tree (KT1T) na shiyyar Daura. Hon. Shafi’u Abdu Duwan zai jagoranci kwamitin shiyar wajen tabbatar da ingantaccen aiwatar da shirin dasa bishiyoyi miliyan 11 a yankunan da ke ƙarƙashin shiyyar Daura, tare da haɗa kai da ƙananan hukumomi, shugabannin gargajiya da na addini, mata, matasa da sauran masu ruwa da tsaki. A matsayinsa na shugaban kwamitin, zai sa ido kan yadda ake aiwatar da shirin, wayar da kan al’umma kan muhimmancin dasa da kare bishiyoyi, tare da tabbatar…
Read More
‘Yan sanda sun kama mutum biyu da zargin taimakon ‘yan bindiga a Katsina

‘Yan sanda sun kama mutum biyu da zargin taimakon ‘yan bindiga a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina 'Yan sanda da haɗin gwiwan 'yan banga sun kama mutane biyu da ake zargi da taimakawa yan bindiga a ƙaramar hukumar Jibiya. A wata sanarwa jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yan sanda a Katsina DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya bayyana cewa sanda suka tare wata Mota ƙirar Volkswagen Golf numba TFA 29 AA. A bincike da suka gudanar sun gano direban motar mai suna Babangida Mohammed Yana ɗauke da wani mai suna Rabi'u Isah da wasu kaya da ake zargi za su kaiwa 'yan bindiga a nan Jibiya. DSP Abubakar Sadiq ya bayyana cewa…
Read More
An gano gawarwaki mutum 30 bayan harin ’yan ta’adda kan masallatai a Neja – Shugaban Borgu

An gano gawarwaki mutum 30 bayan harin ’yan ta’adda kan masallatai a Neja – Shugaban Borgu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kimanin mutane 30 ne suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren da aka kai wa masu ibada a lokacin sallar Juma’a a ƙananan hukumomin Borgu na Jihar Neja, yayin da aka yi awon gaba da sama da mutum 60, a cewar Shugaban Ƙƙaramar Hukumar Borgu, Mohammed Abdullahi. Abdullahi ya ce, maharan sun sace sama da mutum 60 daga masallatai daban-daban a ƙauyuka huɗu, yayin da suke gudanar da sallar Juma’a a ranar Juma’ar da ta gabata. Wannan bayani ya zo ne bayan Shugaban ƙasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi Allah-wadai da sace ɗimbin masu ibadar, tare da…
Read More
EFCC ta saka tukwicin kashi biyar ga masu kwarmaton ɓoye dukiyar Nijeriya a ƙasashen waje

EFCC ta saka tukwicin kashi biyar ga masu kwarmaton ɓoye dukiyar Nijeriya a ƙasashen waje

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Hukumar Yaƙi da Masu Yi wa Tattalin Arziƙin ƙasa Zagon ƙasa (EFCC), Mista Ola Olukoyede, ya yi alƙawarin bai wa masu fallasa bayanai a faɗin duniya lada tsakanin kashi 2.5 zuwa 5 cikin 100 ga duk wanda ya bayar da sahihin bayani da zai taimaka wajen gano tare da kwato kuɗaɗe ko dukiyoyin Nijeriya da ake zargin ’yan Nijeriya masu rashawa sun wawashe suka kai ƙasashen waje. Olukoyede ya yi wannan kiran ne ranar Laraba yayin gabatar da jawabi a taron ƙasa da ƙasa karo na 43 kan laifukan tattalin arziki da aka…
Read More
’Yan sandan Abuja sun ƙaryata rahoton sayar da ƙodar matasa a Nyanya

’Yan sandan Abuja sun ƙaryata rahoton sayar da ƙodar matasa a Nyanya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta ƙaryata wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta, wanda ke iƙirarin cewa matasan da ke zaune a yankin Nyanya sun sayar da ƙodarsu domin samun kuɗi, yayin da wani wakili a Mararaba ke sayen sassan jikin mutane. Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar ’yan sandan FCT, SP Josephine Adeh, ta bayyana a Abuja ranar Laraba cewa rundunar ba ta samu ko tabbatar da wani rahoto makamancin haka ba. Ta ce babu wata sanarwa ko saƙo da ya fito daga rundunar da ke tabbatar da…
Read More
Gwamnatin Kano ta ƙara mafi ƙarancin fansho daga N5,000 zuwa N20,000

Gwamnatin Kano ta ƙara mafi ƙarancin fansho daga N5,000 zuwa N20,000

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano ta ƙara mafi ƙarancin kuɗin fanshon da ake biyan ma’aikatan da suka yi ritaya daga N5,000 zuwa N20,000 a wata. Shugaban ƙungiyar ’Yan Fansho ta Nijeriya (NUP), reshen Jihar Kano, Shuaib Musa-Jibrin, ne ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) a Kano. Musa-Jibrin ya ce ƙarin kuɗin fanshon ya biyo bayan tattaunawa tsakanin gwamnatin jihar da wakilan ’yan fansho. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Kano ta samu ci gaba wajen biyan basussukan alawus-alawus da sauran hakkokin ’yan fansho. A cewarsa, daga cikin bashin da aka gada…
Read More
Kyamar baƙi: Ghana ta ƙi karɓar tallafin MTN na miliyan GH¢20 ga ’yan ƙasarta

Kyamar baƙi: Ghana ta ƙi karɓar tallafin MTN na miliyan GH¢20 ga ’yan ƙasarta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin GH¢20 miliyan (kimanin Naira biliyan 2.4) da kamfanin MTN ya yi niyyar bayarwa domin tallafa wa ’yan Ghana da hare-haren kyamar baƙin fata suka shafa a Afirka ta Kudu. Ma’aikatar Harkokin Wajen Ghana ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, inda ta ce gwamnatin ƙasar ta riga ta tanadi isassun kuɗaɗe domin kwashe ’yan Ghana da abin ya shafa daga Afirka ta Kudu da kuma taimaka musu wajen komawa rayuwa bayan dawowarsu. Ya zuwa yanzu, gwamnatin Ghana ta kwashe sama da ’yan kasarta…
Read More
Ndume ya buƙaci Tinubu ya kori ‘marasa ƙwarewa’ daga gwamnatinsa

Ndume ya buƙaci Tinubu ya kori ‘marasa ƙwarewa’ daga gwamnatinsa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sanata mai wakiltar Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya cire jami’an da ba su da kwarewa daga cikin gwamnatinsa, yana mai cewa kasancewarsu na jawo wa gwamnatin abin kunya. Ndume, wanda tsohon shugaban marasa rinjaye ne a Majalisar Dattawa kuma jigo a jam’iyyar APC, ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Arise Tɓ. Ya ce abin da ya kira “kakistrocrats”, wato mutanen da ba su da kwarewa ko cancantar gudanar da mulki, na taka muhimmiyar rawa wajen haifar da rikice-rikice da badakalar da…
Read More