ukarofi

11000 Posts
An tabbatar da sarautar Sarkin Kudun Illela ga Alhaji Usman Yakubu

An tabbatar da sarautar Sarkin Kudun Illela ga Alhaji Usman Yakubu

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamnatin jihar kebbi ta tabbatar da sarautar uban Ƙasar Kudun Illela da ke masarautar Yauri ga Alhaji Usman Yakubu. Wannan na ƙunshe ne a wata takarda mai ɗauke da sa hannun kwamishinan ƙananan hukumomi da masarautu Honarabul Abubakar Umar Dutinmari da aka rabawa manema labarai ranar Juma'a.Takardar ta bayyana cewa naɗin ya biyo bayan rasuwar Hakimin Illela, Aliyu Adam watannin baya da suka wuce. Umar-Dutsinmari ya bayyana cewa Majalisar Masarautar Yauri ta karɓi takardu daga ƴan takarar neman wannan sarautar har guda 20 daga ahalin da suka gaji wannan sarautar tun bayan rasuwar tsohon basaraken.…
Read More
Injiniya Rabi’u ya raba takin zamani buhu 200 ga al’ummar yankin Burdugau a Katsina

Injiniya Rabi’u ya raba takin zamani buhu 200 ga al’ummar yankin Burdugau a Katsina

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Al’ummar garin Burdugau da ke ƙaramar hukumar Malumfashi a Jihar Katsina da al’ummomin da ke kewaye da su sun yaba da wani mai taimakon al’umma, Injiniya Muhammad Rabi’u Hashim, bayan gudanar da babban taron tallafawa ga manoma, mata masu aure, da kuma marasa lafiya a yankin. A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin al’umma, mazauna yankin sun bayyana godiyarsu bisa wannan alheri da suka ce ya zo daidai lokaci kuma ya yi tasiri ga rayuwar alummar yankin. A cewar al’ummar, Injiniya Rabi'u Hashim ya bayar da buhunan taki guda 200 kimani Naira miliyan…
Read More
Wata mata ta ɓoye kwarto cikin jakar Ghana-must-go a Kebbi

Wata mata ta ɓoye kwarto cikin jakar Ghana-must-go a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Jami’an hukumar Hisbah ta jihar Kebbi sun kama wani mutum da aka gano yana ɓoye a cikin ƙaton buhun nan na "Ghana-Must-Go" a gidan wata matar aure da ke unguwar Badariya a birnin Kebbi. Daraktan Shari’a na hukumar Malam Sirajo Kamba, ya bayyana cewa hukumar ta kai samame ne a gidan bayan samun bayani ne daga mazauna unguwar ne inda suka sandar da hukumar cewa sun ga wani mutum ba su yarda da salon da ya ɗauka na shiga gidan ba da misalin ƙarfe 12:15 na daren ranar Litinin ɗin da ta gabata sai suka…
Read More
Yawancin mutanen Amurka suna rayuwar hannu-baka-hannu-ƙwarya, inji mazaunin ƙasar

Yawancin mutanen Amurka suna rayuwar hannu-baka-hannu-ƙwarya, inji mazaunin ƙasar

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani ɗan kasuwar Nijeriya kuma mai harkar bunƙasa gidaje da ke zaune a Amurka, Femi Rogers, ya yi kira ga matasan Nijeriya da ke kallon ƙaura zuwa ƙasashen waje a matsayin mafita ta samun sauƙin rayuwa da su sake nazari, yana mai cewa rayuwa a Amurka ba ta da sauƙin kuɗi kamar yadda mutane da dama ke zato. Rogers ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a shirin Frankly Business Podcast, inda ya ce tsadar gidaje, haraji, kuɗin wutar lantarki, ruwa da sauran kuɗaɗen rayuwa na sanya mutane da dama a Amurka rayuwa daga abin da…
Read More
NATO ta zaɓi jiragen leƙen asirin Saab na Sweden, ta yi watsi da tayin Boeing na Amurka

NATO ta zaɓi jiragen leƙen asirin Saab na Sweden, ta yi watsi da tayin Boeing na Amurka

Matakin ya zo ne yayin da Trump ke ci gaba da matsa wa ƙawayen NATO su ƙara kashe kuɗi kan tsaro da kuma sayen makaman Amurka. ƙungiyar tsaron ƙasashen Arewacin Tekun Atlantika (NATO) ta sanar da wani shiri na kusan dala biliyan 4.5 domin sayen sabbin jiragen leƙen asiri da gargaɗin barazana na GlobalEye, waɗanda kamfanin Saab na ƙasar Sweden ta ƙera. Matakin ya nuna cewa ƙungiyar ta fifita fasahar Sweden kan ta kamfanin Boeing na Amurka wajen maye gurbin tsofaffin jiragen AWACS da suka yi shekaru da dama suna aiki. Sanarwar ta fito ne a yayin taron ƙasashen NATO…
Read More
Trump ya soki Firaministar Italiya kan rikicin Iran, duk da cewa ya ce “mutumiyar kirki ce”

Trump ya soki Firaministar Italiya kan rikicin Iran, duk da cewa ya ce “mutumiyar kirki ce”

Gwamnatin Italiya ta zaɓi yin shiru domin kare dangantaka da Amurka, yayin da ake sa ran shugabannin biyu za su haɗu a taron NATO. Sabuwar takun-saƙa ta ɓarke tsakanin Shugaban Amurka, Donald Trump, da Firaministar Italiya, Giorgia Meloni, bayan shugaban na Amurka ya zargi Meloni da ƙin ba Washington goyon baya a rikicin da ake yi da Iran. Duk da cewa Trump ya bayyana Meloni a matsayin "mutumiyar kirki", ya ce rashin amincewarta ta shiga cikin ƙoƙarin da Amurka ke yi game da Iran ya janyo tsaiko a kyakkyawar dangantakar da ke tsakaninsu. Trump ya yi waɗannan kalamai ne yayin…
Read More
Ghana ta ɗage taron haɗin gwiwa da Afirka ta Kudu saboda hare-haren ƙyamar baƙi

Ghana ta ɗage taron haɗin gwiwa da Afirka ta Kudu saboda hare-haren ƙyamar baƙi

Gwamnatocin Ghana da Afirka ta Kudu sun ce dangantakarsu na nan daram duk da jinkirta taron haɗin gwiwa. Gwamnatin ƙasar Ghana ta sanar da ɗage taron haɗin gwiwa da aka shirya gudanarwa da Afirka ta Kudu a watan Agusta, saboda yadda hare-haren da ake kai wa baƙin haure a ƙasar ta Afirka ta Kudu suka ƙara ƙamari a cikin 'yan watannin nan. Mai magana da yawun gwamnatin Ghana, Feliɗ Kwakye Ofosu, ya bayyana cewa idan aka gudanar da taron a halin da ake ciki yanzu, tabbas batun hare-haren ƙyamar baƙi ne zai mamaye tattaunawar, maimakon muhimman batutuwan haɗin gwiwar da…
Read More
NDLEA ta kama tsohuwa ’yar shekara 67 da hodar iblis ɓoye cikin ɓawon ayaba

NDLEA ta kama tsohuwa ’yar shekara 67 da hodar iblis ɓoye cikin ɓawon ayaba

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta sanar da kama wata tsohuwa mai shekaru 67 mai zama ’yar Nijeriya da Birtaniya, bayan jami’anta sun gano kilogiram 13 na hodar iblis da aka ɓoye cikin ɓawon ayaba na jabu, aka haɗa su da kayan abinci a cikin jakarta a Filin Jirgin Sama na ƙasa da ƙasa na Murtala Muhammed da ke Legas. A cewar hukumar, wadda ta bayyana hakan cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi, an kama wacce ake zargin, mai aikin kula da tsofaffi a Birtaniya, a harabar tashi ta Terminal 2, yayin da…
Read More
Ina samun aƙalla miliyan N2 a duk wata, inji wata mai gashin masara

Ina samun aƙalla miliyan N2 a duk wata, inji wata mai gashin masara

Wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta na wata mai sana'ar gashin masara da ta yi iƙirarin cewa tana samun sama da naira miliyan 2.5 a kowane wata ya jawo cece-kuce a tsakanin 'yan Nijeriya, inda wasu suka nuna shakku kan iƙirarin, yayin da wasu kuma suka ce hakan na iya yiwuwa idan kasuwancin yana gudana a wuri mai kyau kuma ana tafiyar da shi yadda ya kamata. A cikin gajeren bidiyon da ya karaɗe shafukan sada zumunta daban-daban, an ga wata mata tana tambayar mai sayar da masarar yawan kuɗin da take samu daga sana'arta. Da amsa…
Read More
Dalilin da ya sa ba zan auri abokin sana’ata ta fim  ba – Rahama Sidi Ali

Dalilin da ya sa ba zan auri abokin sana’ata ta fim  ba – Rahama Sidi Ali

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano  Fitacciyar jarumar Kannywood, Rahama Sidi Ali, wacce ta yi fice sosai a Arewacin Najeriya sakamakon rawar da ta taka a  matsayin Umma, uwa mai tausayi da hikima ga Maryam a cikin shahararren shirin fim ɗin 'Labarina'. Duk da cewa tana da ƙarancin shekaru, idan aka kwatanta da irin rawar da take takawa, yadda take fitowa a matsayin uwa ya sa ta samu karɓuwa da yabo daga miliyoyin masu kallo. A wannan hira da wakilin Blueprint Manhaja a Kano, Ibrahim Hamisu ya yi da  Rahama Sidi Ali ya yi waiwaye kan rawar da ta taka  a…
Read More