29
Aug
Daga SULEIMAN HUSSAINI D/KUDU a Kano A Kano, Mai Martaba Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Umar Isa (Autan Bawo), ya naɗa ɗansa a matsayin Chiroman Rano, kuma Hakimin Gundumar Gwamma, tare da ɗaga darajar wasu Dagatai biyu zuwa Hakimai Masu Gunduma. An gudanar da bikin naɗin ne a fadar Sarkin da ke garin Rano ranar Juma’ar da ta gabata. Bikin naɗin ya samu halartar Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf; Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Hon. Abdurrahman Suleiman Kawu Sumaila; ɗan Majalisa mai wakiltar ƙananan hukumomin Rano, Bunkure da Kibiya, Rt. Hon. Kabiru Alasan Rurum; wakilan sarakunan Kano, Karaye…
