ukarofi

11000 Posts
Ƙungiyar Matasan Arewa ta sasanta ƙungiyoyin ’yan daba masu gaba da juna a Kano

Ƙungiyar Matasan Arewa ta sasanta ƙungiyoyin ’yan daba masu gaba da juna a Kano

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wata ƙungiyar matasan Arewa ta Arewa Youth Merger Group (APC) ta samu nasarar sasanta ƙungiyoyin ’yan daba masu gaba da juna a Jihar Kano, a wani yunƙuri na rage rikice-rikicen tituna, satar wayoyin hannu, shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da kuma fashi da makami a sassan jihar. Shirin sulhun ya samu goyon bayan hukumomin tsaro, ƙungiyoyin matasa, sarakunan gargajiya da kuma Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta hanyar manufofin Kano First Agenda. A yayin taron sasancin, Mai Kula da ƙungiyar a Matakin Ƙasa, Hon. Musa Mujahid Zaitawa, ya ƙaddamar da rabon fom na rajista…
Read More
Daliban Bichi sun yaba wa ɗan majalisa Abubakar Kabir kan zuba jari a fannin ilimi

Daliban Bichi sun yaba wa ɗan majalisa Abubakar Kabir kan zuba jari a fannin ilimi

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kungiyar ɗaliban ƙaramar Hukumar Bichi ta gudanar da babban taro a Sakatariyar ƙaramar Hukumar domin bayyana goyon bayanta ga ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bichi, Alhaji Abubakar Kabir Abubakar, bisa irin gudunmawar da yake bayarwa wajen bunƙasa ilimi da tallafa wa ɗalibai a yankin. A cikin wata sanarwa da Jami'ar Yaɗa Labarai ta ƙaramar Hukumar Bichi, Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo, ta fitar, Shugaban ƙungiyar ɗaliban Bichi, Kwamared Mu'azzam Kabiru Adamu, ya bayyana cewa ɗaliban yankin sun gamsu da irin ayyukan ci gaban ilimi da ɗan majalisar ke aiwatarwa, yana mai cewa lokaci ya yi da za…
Read More
Galadiman Legas ya nemi matasa su zage damtse wajen neman ilimi da koyon sana’o’i

Galadiman Legas ya nemi matasa su zage damtse wajen neman ilimi da koyon sana’o’i

Daga DAUDA USMAN a Legas Galadiman Legas, Alhaji Aliyu Bambado, ya yi kira ga matasan Arewacin Nijeriya da ma na ƙasar baki ɗaya da su ƙara ƙaimi wajen neman ilimin zamani da na addini tare da koyon sana’o’in hannu domin samun damar dogaro da kai da kuma inganta rayuwarsu. Galadiman ya bayyana hakan ne yayin da yake karɓar baƙuncin wasu gungun matasa daga unguwanni daban-daban na jihohin Legas da Ogun, waɗanda suka kai masa ziyarar gaisuwa tare da taya shi murnar zagayowar Babbar Sallah ta bana lafiya. Da yake jawabi bayan kammala karɓar baƙuncin nasu, Alhaji Aliyu Bambado ya nuna…
Read More
Hauhawar farashi da tsadar rayuwa sun durƙusar da dubban kasuwanci a Nijeriya – ’Yan kasuwa

Hauhawar farashi da tsadar rayuwa sun durƙusar da dubban kasuwanci a Nijeriya – ’Yan kasuwa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shekaru uku bayan gwamnatin tarayya ta yi alƙawarin samar da asusun tallafi na Naira biliyan 200 domin rage tasirin sauye-sauyen tattalin arziki ga masana’antu da ƙananan ’yan kasuwa, masu ruwa da tsaki sun bayyana cewa har yanzu yawancin waɗanda aka yi niyyar tallafawa ba su amfana da shirin ba. A lokaci guda kuma, miliyoyin ƙananan kasuwanci sun durƙushe tare da rufe ƙofofinsu. Kungiyar Masu ƙananan Kasuwanci ta Nijeriya (ASBON) ta ce kusan ƙananan kasuwanci miliyan biyu ne suka rufe tsakanin shekarun farko uku na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sakamakon cire tallafin man fetur, sauye-sauyen tsarin…
Read More
2027: Kiristocin Neja sun nemi a ba su kujerar mataimakin gwamna

2027: Kiristocin Neja sun nemi a ba su kujerar mataimakin gwamna

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Kiristocin Jihar Neja ƙarƙashin inuwar Coalition of Concerned Christian Stakeholders sun bukaci Gwamna Mohammed Umaru Bago da ya zaɓi ɗan takarar Kirista a matsayin mataimakinsa a zaɓen gwamnan jihar na shekarar 2027. ƙungiyar ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da ta gudanar a Minna ranar Talata, inda ta ce an daɗe ana nuna wa Kiristoci wariya a harkokin mulki da shugabanci a jihar. Ta ce, "Muna kira ga gwamna da shugabannin jam'iyyar APC da su tabbatar da fitowar ɗan takarar mataimakin gwamna daga cikin Kiristoci a zaɓen 2027. Muna ƙin amincewa…
Read More
2027: Dan takarar gwamnan ADC a Kaduna ya gana da El-Rufai, ya ƙara ƙaimi wajen dabarun siyasa

2027: Dan takarar gwamnan ADC a Kaduna ya gana da El-Rufai, ya ƙara ƙaimi wajen dabarun siyasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Dan takarar gwamnan Jihar Kaduna na Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC), Rt. Hon. Isa Ashiru Kudan, ya ƙara zage damtse wajen gudanar da shawarwari da tattaunawar siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ya gana da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, da kuma ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Kaduna ta Arewa, Hon. Mohammed Bello El-Rufai. Ashiru ya gana da tsohon gwamnan ne a ranar Talata, kwanaki kaɗan bayan ya karɓi baƙuncin Bello El-Rufai a wata ziyarar ban girma. Ya bayyana cewa jam'iyyar ADC ta shirya tsaf domin ƙalubalantar jam'iyyar APC mai mulki…
Read More
Kotu ta tanadi hukunci kan ƙorafe-ƙorafen farko a ƙarar Usman Garry kan takarar Pantami

Kotu ta tanadi hukunci kan ƙorafe-ƙorafen farko a ƙarar Usman Garry kan takarar Pantami

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Gombe ta tanadi ranar yanke hukunci kan ƙorafe-ƙorafen farko (preliminary objections) da waɗanda ake ƙara suka gabatar a shari'ar da Usman Aliyu Garry ya shigar yana ƙalubalantar fitowar Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami a matsayin ɗan takarar gwamnan jam'iyyar PDP a zaɓen Gombe na shekarar 2027. A zaman da aka ci gaba da yi ranar Juma'a a gaban Mai Shari'a Amina Aliyu Mohammed, lauyan jam'iyyar PDP, Barista S. M. Yusuf, ya sanar da kotun cewa ya daidaita buƙatarsa ta hanyar gabatar da roƙon baki. Daga nan ya amince…
Read More
Ambaliyar ruwa: SEMA ta gargaɗi al’ummar Faduma a Katsina su fice daga ƙauyen

Ambaliyar ruwa: SEMA ta gargaɗi al’ummar Faduma a Katsina su fice daga ƙauyen

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Katsina (SEMA) ta yi kira ga al'ummar garin Faduma da ke ƙaramar hukumar Rimi da su gaggauta barin gidajensu domin kauce wa barazanar ambaliyar ruwa da ake hasashen za ta afku kafin ƙarshen watan Yuli. Shugabar hukumar SEMA, Hajiya Binta Hussaini Dangani, ta bayyana haka a lokacin da ta kai ziyarar duba halin da al'ummar garin na Faduma suke ciki na fargabar faruwar ambaliyar ruwan zama da masu hasashen yanayi suka yi. Ta ce "Masu hasashen yanayi sun nuna cewa akwai ƙananan hukumomi 14 a Jihar Katsina da…
Read More
Aminu Jaji ya yaba da sake tsayar da Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na 2027

Aminu Jaji ya yaba da sake tsayar da Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na 2027

Daga SANUSI MUHAMMAD Gusau Ɗan Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Dr. Aminu Sani Jaji, ya bayyana sake tsayar da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima a matsayin abokin takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027 a matsayin babban ƙwarin gwiwa ga damar jam’iyyar All Progressives Congress APC a zaɓen. A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis kuma Jamilu Iliyasu Birnin Magaji, mataimakin sa na yaɗa labarai ne ya sanya hannu, Jaji ya ce wannan shawara ta tabbatar da alƙiblar gwamnati kuma alama ce ta ci gaba ga APC gabanin babban zaɓen 2027. Dr. Jaji, wanda ke…
Read More
Har yanzu mutane 79 na hannun ‘yan ta’adda – Ndume ga sojoji bayan ceto ‘yan Oyo

Har yanzu mutane 79 na hannun ‘yan ta’adda – Ndume ga sojoji bayan ceto ‘yan Oyo

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanata Ali Ndume na Borno ta Kudu, ya yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi wajen ceto mutanen mazaɓarsa da har yanzu suke hannun ‘yan ta’adda. Ndume ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na Channels a ranar Juma'a. Ya ce, duk da nasarar ceto ɗalibai da malamai da aka sace a Jihar Oyo daga ɓangaren dakarun tsaro, har yanzu akwai sama da mutane 42 da aka sace a mazaɓarsa, yayin da wasu fiye da 80 kuma ke cigaba da zama a hannun masu garkuwa da su. Don haka…
Read More