ukarofi

11000 Posts
Ruftawar zauren majalisar dokokin Gombe ya yi ajalin ma’aikataci da raunata bakwai

Ruftawar zauren majalisar dokokin Gombe ya yi ajalin ma’aikataci da raunata bakwai

Mutum ɗaya ya rasu yayin da wasu bakwai suka jikkata sakamakon ruftawar wani sashi na sabon ginin Majalisar Dokokin Jihar Gombe da ke ƙarƙashin gini. Al'amarin ya faru ne ranar Juma’a bayan wani ɓangaren rufin mashigar ginin da ake ginawa ya rushe a wurin aikin. Babban Sakataren Ma’aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri ta Jihar Gombe, Ɗanladi Adams, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce mutum ɗaya daga cikin ma’aikatan ya mutu nan take, yayin da sauran bakwai suka samu raunuka daban-daban. Ya bayyana cewa, biyar daga cikinsu na karɓar magani a Asibitin Kwararru na Jihar Gombe, yayin da sauran…
Read More
Idan aka halaka ni, Amurka za ta shafe ku a doron ƙasa – Trump ga Iran bayan jana’izar Ali Khamenei

Idan aka halaka ni, Amurka za ta shafe ku a doron ƙasa – Trump ga Iran bayan jana’izar Ali Khamenei

Shugaba Donald Trump na Amurka ya gargaɗi Iran da cewa za ta fuskanci mummunan martanin sojin ƙasarsa matuƙar ta yi yunƙurin halaka shi ko kai masa wani hari. A wani saƙo da ya wallafa a dandalinsa na Truth Social, Trump ya bayyana cewa ya riga ya bayar da umarnin da suka dace ga hukumomin tsaro, yana mai cewa Amurka ta shirya tsaf domin mayar da martani cikin gaggawa idan aka aiwatar da wata barazana a kansa. Ya yi ikirarin cewa dubban makamai masu linzami suna cikin shiri, yana mai cewa duk wani yunkurin kai masa hari zai jawo farmakin da…
Read More
Tinubu ya umarci a kula da lafiyar ɗalibai da malaman Oyo da aka ceto

Tinubu ya umarci a kula da lafiyar ɗalibai da malaman Oyo da aka ceto

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya bayyana farin cikinsa game da nasarar ceto yara da malaman da aka yi garkuwa da su a ƙauyen Oriire da ke Ogbomoso a Jihar Oyo, yana mai yaba wa Rundunar sojoji, DSS da Rundunar 'Yan sanda kan kawo ƙarshen kwanaki 57 da mutanen suka shafe a komar 'yan bindiga. Shugaban ya ce, atisayen jami'an tsaro ya yi sanadiyyar kama masu garkuwa guda takwas yayin da aka halaka wasu da dama, lamarin da ya sa mutanen suka shaƙi iskar 'yanci da kuma sauƙi ga iyalansu da ƙasa baki ɗaya. A sanarwar…
Read More
Tsawa ta maida ’ya’ya uku marayu a a Jigawa

Tsawa ta maida ’ya’ya uku marayu a a Jigawa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani mummunan al’amari ya auku a ƙauyen Gongo da ke ƙarƙashin gundumar Limawa a ƙaramar hukumar Dutse ta Jihar Jigawa, inda tsawa ta kashe wani mutum mai shekara 30 tare da jikkata yara biyu, lamarin da ya sake tayar da hankalin mazauna yankunan karkara kan haɗarin tsawa da ke yawan faruwa a yankin. Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:15 na yammacin ranar 22 ga Yunin 2026, lokacin da wata guguwar ruwan sama mai ƙarfi tare da tsawa da walƙiya ta afkawa ƙauyen, wanda ke da tazarar kusan kilomita biyar gabashin birnin Dutse. Mamacin, Iliya…
Read More
Odita Janar ya buƙaci a binciki zargin karkatar da Dala miliyan 6.2 a gwamnatin Buhari

Odita Janar ya buƙaci a binciki zargin karkatar da Dala miliyan 6.2 a gwamnatin Buhari

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babban Mai Bincike na Musamman da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa domin gudanar da bincike kan harkokin Babban Bankin Nijeriya (CBN) a zamanin tsohon gwamna Godwin Emefiele, Jim Obazee, ya buƙaci a faɗaɗa binciken shari’ar da ake yi kan zargin karkatar da dala miliyan 6.2 daga asusun musayar kuɗaɗen ƙasashen waje na Gwamnatin Tarayya da ke hannun CBN. Obazee ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da yake ba da shaida a gaban Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya Abuja a madadin Hukumar Yaƙi da Masu Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati (EFCC), a shari’ar da…
Read More
Majalisar Dattawa ta amince da tara tiriliyan N11 a hukumar Kwastom

Majalisar Dattawa ta amince da tara tiriliyan N11 a hukumar Kwastom

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kwamitin Majalisar Dattawa Mai Kula da Harkokin Kwastom da Harajin Kaya ya amince da burin tara kuɗaɗen shiga har Naira tiriliyan 11 ga Hukumar Kwastom ta Nijeriya (NCS) a shekarar kasafin kuɗi ta 2026. Kwamitin ya kuma amince da kasafin kuɗin gudanarwar hukumar na Naira tiriliyan 1.235, yana mai bayyana kwarin gwiwar cewa hukumar za ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen da ta fara tare da ƙara yawan kuɗaɗen shiga duk da ƙalubalen tattalin arzikin duniya. An cimma wannan matsaya ne bayan Babban Kwanturola Janar na Hukumar Kwastom ta Nijeriya, Adewale Adeniyi, ya kare kasafin…
Read More
NIN ce kaɗai sahihiyar shaida  a Nijeriya – Sabuwar dokar NIMC

NIN ce kaɗai sahihiyar shaida  a Nijeriya – Sabuwar dokar NIMC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Hukumar Kula da Shaidar ɗan ƙasa ta ƙasa (NIMC) ta sanar da cewa adadin 'yan Nijeriya da mazauna ƙasar bisa doka da suka yi rajista a Rumbun Bayanai na Shaidar ɗan ƙasa (NIDB) ya haura miliyan 136, yayin da sabuwar Dokar NIMC ta 2026 ta fara aiki a hukumance. Babbar Darakta Janar ta Hukumar NIMC, Injiniya Abisoye Coker-Odusote, ce ta bayyana hakan yayin wata ziyarar girmamawa da ta kai wa Ma’aikatar Tarayya ta Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki a ranar Litinin. Ta bayyana cewa, sabuwar dokar ta soke tsohuwar Dokar NIMC ta 2007, tare da shimfiɗa…
Read More
Nijeriya ta dakatar da aiwatar da sabbin dokokin intanet da fasahar zamani

Nijeriya ta dakatar da aiwatar da sabbin dokokin intanet da fasahar zamani

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ta bada umarnin dakatar da aiwatar da sabbin ƙa'idoji da dokokin da suka shafi dandamalin intanet, masu samar da ayyukan yanar gizo da sauran batutuwan tattalin arzikin zamani, har sai an kammala cikakken nazari da haɗa manufofin ƙasa guda ɗaya a wannan fanni. An bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Ministan Sadarwa, ƙirƙire-ƙirƙire da Tattalin Arzikin Zamani, Bosun Tijani, ya fitar a ranar Talata bayan wata ganawa da shugabannin Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC), Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta ƙasa (NITDA) da kuma Hukumar Kare Bayanai ta Nijeriya (NDPC). Ministan ya ce, an…
Read More
Kiran kanku lauyoyi zai janyo muku kora – Makarantar lauyoyi ga ɗalibanta

Kiran kanku lauyoyi zai janyo muku kora – Makarantar lauyoyi ga ɗalibanta

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Ilimin Shari'a ta Makarantar Lauyoyi ta Nijeriya ta gargaɗi ɗaliban da ke jiran bikin rantsuwar kama aikin lauya, wato bar, da su guji sanya kayan aikin lauya tare da bayyana kansu a matsayin cikakkun lauyoyi kafin a hukumance a karɓe su cikin ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya. Rahoton ya nuna cewa wannan gargaɗi na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakatariyar Majalisar Ilimin Shari'a kuma Daraktar Gudanarwa, Aderonke Osho, ta sanya wa hannu, wadda Makarantar Horar Da Lauyoyi Ta Nijeriya ta fitar a ranar Talata. Majalisar ta bayyana cewa ta lura da yadda wasu masu jiran…
Read More
Sauya sheƙar Ubandoma zuwa APC ta janyo cece-kuce a Sakkwato

Sauya sheƙar Ubandoma zuwa APC ta janyo cece-kuce a Sakkwato

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Sakkwato a zaɓen 2023, Malam Sa’idu Umar Ubandoma, ya fice daga jam’iyyar ADC tare da komawa APC. Wannan ma cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko kan yaɗa labarai, Bashar Abubakar, ya fitar. An ce Sanata Wamakko ne, ya tarɓi Ubandoma zuwa jam’iyyar APC a gidansa da ke Asokoro a Abuja. Ubandoma, wanda ya taɓa riƙe muƙamin Kwamishinan Kuɗi da kuma Sakataren Gwamnatin Jihar Sakkwato a gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal, ya ce salon jagorancin Sanata Wamakko da ayyukan ci gaban da Gwamna Ahmed Aliyu ke…
Read More