28
Aug
Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Dan takarar gwamnan Jihar Kano a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2027, Amb. Muhammad Bello Dalhatu, ya bayyana ƙudirinsa na sake fasalta tafiyar jihar, tare da mai da hankali kan bunƙasa tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa da inganta rayuwar al’umma. Amb. Dalhatu ya ce lokaci ya yi da za a kawo sauyi a Kano, yana mai cewa jihar na buƙatar shugabanci mai hangen nesa, ƙwarewa da kishin jama’a domin amfani da dimbin damar da Allah Ya hore mata. Ya ce yana da burin samar da tsarin shugabanci da zai tunkari matsalolin da suka…
