ukarofi

11670 Posts
2027: Yadda Bello Dalhatu ya fito da sabon tsarin ceton al’ummar Kano

2027: Yadda Bello Dalhatu ya fito da sabon tsarin ceton al’ummar Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Dan takarar gwamnan Jihar Kano a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2027, Amb. Muhammad Bello Dalhatu, ya bayyana ƙudirinsa na sake fasalta tafiyar jihar, tare da mai da hankali kan bunƙasa tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa da inganta rayuwar al’umma. Amb. Dalhatu ya ce lokaci ya yi da za a kawo sauyi a Kano, yana mai cewa jihar na buƙatar shugabanci mai hangen nesa, ƙwarewa da kishin jama’a domin amfani da dimbin damar da Allah Ya hore mata. Ya ce yana da burin samar da tsarin shugabanci da zai tunkari matsalolin da suka…
Read More
Matatar Dangote ta ƙara farashin fetur duk da faɗuwar farashin ɗanyen mai

Matatar Dangote ta ƙara farashin fetur duk da faɗuwar farashin ɗanyen mai

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Duk da raguwar farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya, Matatar Man Fetur ta Dangote ta ƙara farashin fetur, lamarin da ake sa ran zai sa farashin man ya koma kusan Naira 1,250 kan kowace lita. Matatar Man Fetur da Sinadarai ta Dangote (FZE) ta ƙara farashin sayar da man fetur daga Naira 1,185 zuwa Naira 1,200 kan kowace lita. Sabon farashin ya fara aiki ne daga ranar 26 ga Agusta, 2026. Rahotanni sun ce matatar ta sanar da abokan cinikinta da wannan sauyi ne ta wata sanarwa da sashen Ayyukan Kasuwanci na Rukunin Kamfanin ya fitar…
Read More
A ƙidaya kowace haihuwa, a rubuta kowace mutuwa

A ƙidaya kowace haihuwa, a rubuta kowace mutuwa

Rajistar haihuwa da mutuwa ba wani aiki ne na tattara alƙaluma kawai ba. Ita ce ginshiƙin da ƙasa ta zamani ke dogaro da shi wajen fahimtar al’ummarta, tsara buƙatunsu da kuma auna ci gabanta. Idan babu sahihan bayanan haihuwa da mutuwa, hasashen yawan jama’a yana zama cikin rashin tabbas, shirye-shiryen samar da ayyukan more rayuwa su raunana, yayin da manufofin ci gaba ke fuskantar haɗarin ginuwa a kan zato maimakon sahihan bayanai. Saboda haka, ci gaba da gazawar Nijeriya wajen yin rajistar haihuwa da mutuwa abu ne da ya kamata ya damu kowace matakin gwamnati. Binciken Alƙaluman Jama’a da Lafiyar…
Read More
An buƙaci shugabannin ƙananan hukumomi su ja mataimakansu a jiki

An buƙaci shugabannin ƙananan hukumomi su ja mataimakansu a jiki

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe Kwamishinan ƙananan hukumomi da cigaban al’umma na Jihar Gombe, Barista Sani A.A. Haruna, ya buƙaci shugabannin ƙananan hukumomi 11 da na yankunan cigaban ƙananan hukumomi (LCDA) da su riƙa bai wa mataimakansu muhimmiyar rawa wajen tafiyar da harkokin mulki. Haruna ya yi wannan kiran ne a wajen taron ƙara wa juna sani da ma’aikatar ƙananan hukumomi da cigaban al’umma ta shirya domin shugabannin ƙananan hukumomi da LCDA na jihar. Kwamishinan ya ce bai kamata shugabannin su mayar da mataimakansu saniyar ware ba, yana mai cewa sanya su cikin ayyukan gwamnati zai taimaka wajen inganta…
Read More
Miyetti Allah ta karrama Sanata Maidoki

Miyetti Allah ta karrama Sanata Maidoki

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Ƙungiyar Miyetti Allah reshen ƙaramar hukumar Zuru ta karrama Sanata Musa Garba Maidoki Sanata mai wakiltar gundumar Kebbi ta kudu.Shugabannin ƙungiyar miyetti Allah na ƙaramar hukumar ta Zuru sun bayyana cewa ɗan majalisar dattijan ya cancanci wannan karramawar bisa irin gagarumin ƙoƙari da jajircewar da ya ke nunawa wajen tallafa wa harkokin tsaro da zaman lafiya a yankin da ya ke wakilta. An shirya gabatar da wannan karramawa ne jiya yayin bikin taron ƙaddamar da shugabannin yaƙin neman zaɓe na jam’iyyar ADC ne saboda a nuna wa al'ummar jihar Kebbi irin ƙoƙarin da ya ke…
Read More
Zargin sace kayan asibiti: Hukumar NHMB ta kafa kwamitin bincike

Zargin sace kayan asibiti: Hukumar NHMB ta kafa kwamitin bincike

Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Hukumar kula da asibitoci ta jihar Nasarawa (NHMB) ta kafa wani kwamiti domin binciken zargin sace kayayyakin asibitin gwamnati na yankin rayawa na Umaisha dake ƙaramar hukumar Toto a jihar. Bincike a kan lamarin ya tabbatar cewa ɗan majalisar dokokin jihar mai wakiltar mazaɓar Ugya/Umaisha Hon. Ibrahim Sa’ad ne ya bai wa asibitin kayan tallafin don a turo su zuwa Umaisha ɗin amma sai aka gano daga bisani cewa kayayyakin sun yi ɓatan dabo a yanzu haka. Dr. Egba Edego babban daraktan hukumar ne ya bayyana haka yayin da yake magana da manema labarai…
Read More
Sharhin littafin ‘Kurman Hisabi’

Sharhin littafin ‘Kurman Hisabi’

Daga RAHMA SABO USMAN  RUBUTAWA: Ayuba Muhammad Danzaki  (ZAKIN MARUBUTA) SHARHI: Rahma Sabo Usman SHEKARAR BUGU: 2022 Taƙaitaccen Labarin: 'Kurman hisabi' labari ne da aka gina shi a kan jigon 'Kunnen ƙashi'  Labari ne akan wani kangararren yaro mai suna Umar Niga, yaron da ya yi shuhura gurin tujara da kuma ja wo jarfa. Ya kuma taso a irin yanayin nan da ake kira da albasa da ta ƙi yo halin ruwa, domin kuwa duk inda kake neman mutanen kirki iyayensa sun kai har sun kere. A kullum rana iyayensa kan zubar da hawayen takaici da baƙinciki ta sanadiyar ɗan…
Read More
Tunanin Bahaushe game da zalunci: Nazari daga tatsuniyar iccen ƙosai

Tunanin Bahaushe game da zalunci: Nazari daga tatsuniyar iccen ƙosai

Daga SHEHU SANI LERE  Gatanan-gatananku. Wani yaro ne ƙarami mahaifansa suka rasu suka bar shi a wajen ƙanin mahaifinsa, sun bar masa dukiya mai yawa. Sai ƙanin mahaifin ya hau kan dukiyar, sai ya zamo yana azabtar da shi. Ba a bashi isasshen abinci, sai dai kullum a bashi ƙosai ƙwara ɗaya, sauran yaran gida kuma a basu su ci su ƙoshi. Ana anan, sai marayan nan ya shuka ƙosan da ake bashi yana zaga wa kullum yana bashi ruwa har ya tsiro ya zama bishiya babba, tayi 'ya'yan ƙosai da yawa. Idan yaji yunwa, sai ya tafi wajen bishiyar…
Read More
Fiye da mutane biliyan ɗaya ne suke rayuwa a unguwannin awon igiya a duniya — Farfesa Abdulaziz Raji

Fiye da mutane biliyan ɗaya ne suke rayuwa a unguwannin awon igiya a duniya — Farfesa Abdulaziz Raji

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta fara wani taron ƙasa da ƙasa na tsawon kwanaki biyu, wanda Sashen Kimiyyar Ƙasa da Muhalli na jami’ar ya shirya, domin tattauna hanyoyin da za a ƙara sanya al’umma cikin ayyukan yaƙi da sauyin yanayi da kuma samar da birane masu ɗorewa da dacewa da rayuwa. Taron, wanda aka yi shi a sashin kimiyyar Ƙasa na jami'ar wanda shi ne karo na biyu, taken taron na bana shi ne: “Gina makoma mai juriya: Matsugunan da ba a tsara su ba da matakan yaƙi da sauyin yanayi da al’umma…
Read More
Jam’iyyar ADC ta ƙaddamar da jagororin yaƙin neman zaɓe a Kebbi

Jam’iyyar ADC ta ƙaddamar da jagororin yaƙin neman zaɓe a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi A cikin shirin ta na tinkarar babban zaɓen game-gari na shekarar 2027, ranar Laraba ɗin nan jam'iyyar ADC a jihar Kebbi ta ƙaddamar da jagororin yaƙin neman zaɓe. Da ya ke jawabi a wajen taron, ɗan takarar kujerar mataimakin gwamna Dakta Musa Zagi Argungu ya bayyana cewa, sanin kowa ne ya'yan jam'iyyar ADC mutane ne da suka san ya kamata, masu bin doka da oda da son zaman lafiya, saboda haka ne ta ke bin ƙa'idojin da dokokin ƙasa da na zaɓe suka gindaya saboda haka ana fatar za su cigaba da bin doka da…
Read More