11
Jul
Mutum ɗaya ya rasu yayin da wasu bakwai suka jikkata sakamakon ruftawar wani sashi na sabon ginin Majalisar Dokokin Jihar Gombe da ke ƙarƙashin gini. Al'amarin ya faru ne ranar Juma’a bayan wani ɓangaren rufin mashigar ginin da ake ginawa ya rushe a wurin aikin. Babban Sakataren Ma’aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri ta Jihar Gombe, Ɗanladi Adams, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce mutum ɗaya daga cikin ma’aikatan ya mutu nan take, yayin da sauran bakwai suka samu raunuka daban-daban. Ya bayyana cewa, biyar daga cikinsu na karɓar magani a Asibitin Kwararru na Jihar Gombe, yayin da sauran…
