11
Jul
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ƙarfafa yaƙi da matsalar tsaro ta hanyar amfani da fasahar zamani, inganta tattara bayanan sirri da kuma ƙara wa rundunar sojojin ƙasar ƙarfi. Tinubu, wanda mataimakinsa, Kashim Shettima, ya wakilta a bikin Ranar Sojin Nijeriya ta 2026 da aka gudanar a Fatakwal, ya ce gwamnati na ci gaba da zuba jari wajen samar da sabbin kayan aikin soja da kuma horar da jami’ai domin su tunkari sabbin barazanar tsaro. Ya ce gwamnati za ta kuma bunƙasa bincike da ƙera kayan aikin soja a cikin…
