ukarofi

11000 Posts
Za mu yi amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da matsalar tsaro – Tinubu

Za mu yi amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da matsalar tsaro – Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ƙarfafa yaƙi da matsalar tsaro ta hanyar amfani da fasahar zamani, inganta tattara bayanan sirri da kuma ƙara wa rundunar sojojin ƙasar ƙarfi. Tinubu, wanda mataimakinsa, Kashim Shettima, ya wakilta a bikin Ranar Sojin Nijeriya ta 2026 da aka gudanar a Fatakwal, ya ce gwamnati na ci gaba da zuba jari wajen samar da sabbin kayan aikin soja da kuma horar da jami’ai domin su tunkari sabbin barazanar tsaro. Ya ce gwamnati za ta kuma bunƙasa bincike da ƙera kayan aikin soja a cikin…
Read More
Majalisar Wakilai ce ta saka ayyukan titina a kasafin kuɗin Hukumar Almajirai — NCAOOSCE

Majalisar Wakilai ce ta saka ayyukan titina a kasafin kuɗin Hukumar Almajirai — NCAOOSCE

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Hukumar Kula da Ilimin Almajirai da Yara Marasa Zuwa Makaranta ta ƙasa (NCAOOSCE) ta bayyana cewa ayyukan gina titina da wasu ayyuka da suka bayyana a cikin kasafin kuɗinta na shekarar 2026 ba daga cikin ainihin ayyukan da aka kafa hukumar domin gudanarwa ba ne, illa ayyukan maza u da Majalisar Tarayya ta ɗora mata alhakin aiwatarwa. Hukumar ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da mai ba Babban Sakataren Hukumar shawara kan harkokin yaɗa labarai da sadarwa, Malam Nura Muhammad, ya fitar a ranar Talata a Abuja. Tun da farko, Blueprint Manhaja ta…
Read More
Zargin ƙirƙirar hukumar bogi: Gwamnatin Tinubu na yunƙurin kare Gbajabiamila – Atiku

Zargin ƙirƙirar hukumar bogi: Gwamnatin Tinubu na yunƙurin kare Gbajabiamila – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya ce ƙoƙarin da Fadar Shugaban ƙasa ta yi na kare Shugaban Ma’aikatanta, Femi Gbajabiamila, daga zarge-zargen da ake yi masa ya ƙara jefa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu cikin abin kunya. A cikin wata sanarwa, Atiku ya yi zargin cewa Kasafin Kuɗin 2026 ya ƙunshi tanade-tanaden da suka karkatar da biliyoyin naira zuwa ayyukan gina hanyoyi ta hannun Hukumar Kula da Ilimin Almajirai da Yaran da ba sa zuwa makaranta, duk da cewa ba haka aikin hukumar yake ba. Ya ce hakan na nuna yadda ake ɓoye ayyuka…
Read More
2027: Ko ni ba na tsoron Obi balle Tinubu, inji Umahi

2027: Ko ni ba na tsoron Obi balle Tinubu, inji Umahi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Ministan ayyuka, David Umahi, ya ce tsohon ɗan takarar Shugaban ƙasa na Jam'iyyar LP, Peter Obi, ba ya zama barazana ga Shugaba Bola Tinubu ko Jam'iyyar APC a zaɓen 2027. Umahi, yayin wata hira da Arise TV a ranar Talata, ya ce bai ma tsoron Obi ba, balle Shugaba Tinubu, yana mai zargin cewa ƙarfin siyasar Obi ya samo asali ne daga yaɗa labarai a kafafen sada zumunta fiye da ainihin tasirinsa. Ministan ya kuma soki wa'adin shekaru takwas da Obi ya yi a matsayin gwamnan Jihar Anambra, yana zarginsa da kasa gyara hanyoyi,…
Read More
Abin da ya sa gwamnatin Zamfara ta hana al’umma sulhu da ‘yan bindiga

Abin da ya sa gwamnatin Zamfara ta hana al’umma sulhu da ‘yan bindiga

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  A Nijeriya, gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin kasar ta gargadi al'ummar jihar game da yin sulhu da yanbindiga masu garkuwa da mutane. Gwamnatin ta ce duk wanda ya yi sulhu da yanbindiga ya yi gaban kansa tare da nanata cewa ba za ta yi sulhu da yan fashin daji da suka addabi jihar ba. Gwamnatin ta kara jaddada hakan ne bayan wasu dattawa a yankin Maradun kusan 40 sun kubuta daga hannun yanbindiga bayan sun je yin sulhu da yanbindigan. A tattaunawarsa da BBC, shugaban karamar hukumar Talatar Mafara, Yahaya Abubakar…
Read More
DSS ta bayyana yadda matar wani da ake zargi da ta’addanci ke sayen harsasai tana kai masa

DSS ta bayyana yadda matar wani da ake zargi da ta’addanci ke sayen harsasai tana kai masa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jami'in Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), Mista Babatunde Afolabi, ya shaida wa Babbar Kotun Tarayya da ke Ibadan cewa Asmau Omar, daya daga cikin wadanda ake tuhuma a shari'ar safarar makamai ba bisa ka'ida ba, na saye tare da kai wa mijinta harsasai a maboyarsa. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya tuna cewa Asmau Omar da wasu mutum uku suna fuskantar tuhume-tuhume guda 15 da suka hada da hada baki, safarar harsasai ba bisa ka'ida ba, da kuma taimakawa ayyukan ta'addanci. Sauran wadanda ake tuhumar sun hada da Olamide Okesola, Emmanuel Olatunji…
Read More
Kin jinin baƙar fata: Majalisar Dattawa ta yi barazanar yanke hulɗar diflomasiyya da Afirka ta Kudu

Kin jinin baƙar fata: Majalisar Dattawa ta yi barazanar yanke hulɗar diflomasiyya da Afirka ta Kudu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Majalisar Dattawan Nijeriya ta yi gargaɗin cewa ƙasar za ta iya sake duba dangantakarta ta diflomasiyya da Afirka ta Kudu idan hare-haren ƙiyayya ga baƙi, musamman 'yan Nijeriya, suka ci gaba a ƙasar. Wannan matsaya ta biyo bayan wata sanarwa da Sanata Asuƙuo Ekpeyong ya gabatar a zauren majalisar, inda ya jawo hankalin sanatoci kan wa'adin da aka ce an bai wa 'yan Nijeriya mazauna Afirka ta Kudu ranar 30 ga Yunin 2026, lamarin da ya bayyana a matsayin babbar barazana ga rayukansu da hanyoyin samun abincinsu. Majalisar ta nuna damuwa kan yadda hare-haren…
Read More
Kotu ta ba da umarnin ƙwace kadarorin tsohon Ministan wutar lantarki, Saleh Mamman

Kotu ta ba da umarnin ƙwace kadarorin tsohon Ministan wutar lantarki, Saleh Mamman

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Babbar Kotun Tarayya da ke Maitama a Abuja ta ba da umarnin ƙwace wasu kadarori biyar mallakin tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, wanda ke zaman hukuncin daurin shekara 75 bisa laifukan cin hanci da rashawa. Alƙali James Omotosho ya bayar da umarnin ne a ranar 2 ga Yuli, inda ya amince da ƙwace ginin Walijam Apartments da ke Wuse 2, Abuja har abada, bayan ya yanke cewa hukumar EFCC ta tabbatar an saye shi da kuɗaɗen da aka samu ta haramtacciyar hanya. Sauran kadarori huɗu da kotun ta bayar da umarnin ƙwace su…
Read More
An buƙaci masu ruwa da tsaki da su sa baki kan taɓarɓarewar hanyoyin Gwamnatin Tarayya a Katsina

An buƙaci masu ruwa da tsaki da su sa baki kan taɓarɓarewar hanyoyin Gwamnatin Tarayya a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Kungiyar cigaban Funtua tayi kira ga Gwamna Dikko Raɗɗa, 'yan majalisar ƙasa,Sarakuna, manyan 'yan kasuwa da sauran masu faɗa a ji da su buƙaci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya bada umurnin gyaran honyoyin gwamnatin tarayya tun kafin damina ta tafi da wasu. Shugaban ƙungiyar kwamred Mannir Suleiman wanda yayi wannan kira a Funtua a hira da manema labarai ya ce babu wata hanya ta gwamnatin tarayya a Katsina da bata lalace ba. Kwamred Suleiman ya nuna rashin jin daɗin sa ga yadda gwamnatin tarayya ta zuba makudan kuɗi kan gyaran wasu hanyoyi a wasu…
Read More
Hukunta ‘yan ta’adda 150 cikin kwanaki biyu ya nuna sauyin salo a yaƙi da matsalar tsaro

Hukunta ‘yan ta’adda 150 cikin kwanaki biyu ya nuna sauyin salo a yaƙi da matsalar tsaro

Samun nasarar hukunta mutum 150 da aka samu da laifukan ta'addanci cikin kwanaki biyu kacal ya zama wani babban ci gaba a tsarin shari'ar Nijeriya. Wannan mataki ya nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta fara ɗaukar yaƙi da ta'addanci da muhimmanci, tare da ƙoƙarin tabbatar da cewa masu aikata irin waɗannan manyan laifuka sun fuskanci hukunci cikin gaggawa. Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi, ya bayyana cewa a sabon zagayen shari'ar da aka gudanar a Abuja, an saurari shari'o'i kusan 160, inda aka samu hukuncin ɗaurin laifi ga kusan mutum 150. Ya kuma buƙaci al'umma su ci gaba da…
Read More