ukarofi

11670 Posts
DA ƊUMI-ƊUMI: ‘Yan bindiga da dama sun halaka, an raunata sojoji biyu a harin Sifawa

DA ƊUMI-ƊUMI: ‘Yan bindiga da dama sun halaka, an raunata sojoji biyu a harin Sifawa

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Rahotanni daga garin Sifawa a ƙaramar hukumar Bodinga da ke jihar Sokoto sun bayyana cewa yan bindiga da dama sun mutu yayin da sojoji biyu suka sami raunuka a wani artabu tsakanin sojoji da yan bindiga safiyar Laraba ɗin nan. Wani ganau ya labartawa wakilin Jaridar Blueprint Manhaja da cewa ana hasashen maharan sun taso ne daga maɓoyar su da ke jejin ƙauyen Horo a karamar hukumar Shagari da zummar mamayar wata ƙaramar barikin sojoji da ke garin Sifawa sai dai ko da suka kunno kai suka tarar sojojin suna cikin shirin ko ta kwana…
Read More
An gudanar da bikin hawan Gani a Daura

An gudanar da bikin hawan Gani a Daura

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, na daga cikin ɗimbin jama'a da suka halarci hawan Gani da aka gudanar a Masarautar Daura. Wani gagarumin biki na gargajiya da ake gudanarwa duk shekara a matsayin wani ɓangare na bukukuwan tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW). Hawan Gani na daga cikin muhimman al’adun Masarautar Daura, inda sarakuna, hakimai, dagatai, masu unguwanni da sauran al’umma ke fitowa cikin ƙayatattun kayan gargajiya domin nuna al’adun masarautar tare da yin murnar wannan rana mai albarka. Haka kuma makaɗa da mawaƙan gargajiya,wasan Kokawa da damben gargajiya na da…
Read More
Gwamna Sule ya rantsar da sabbin kwamishinoni takwas da sakatarori shida

Gwamna Sule ya rantsar da sabbin kwamishinoni takwas da sakatarori shida

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gwamnan jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule ya rantsar da sabbin kwamishinoni takwas a matsayin mambobin majalisar zartarwar jihar. Gwamnan ya kuma rantsar da sabbin sakatarori na dindindin kuda shida da sabbin masu bashi shawarwari na musamman guda 11 da wani mamba na hukumar kula da ayyukan shari’a ta jihar da kuma wani mamba na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar da akafi sani da NASIEC duk a yau Laraba 26 ga watan Augusta na shekarar 2026 da ake ciki a Lafiya babban birnin jihar. A taron rantsarwar gwamna Sule ya buƙaci su rungumi…
Read More
Gidauniyar Sultan ta yi niyyar yi wa yara 80,772 rigakafi a Zamfara

Gidauniyar Sultan ta yi niyyar yi wa yara 80,772 rigakafi a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Gidauniyar Sultan watau Sultan Foundation, ta ƙaddamar da wani babban shirin rigakafi a Jihar Zamfara da nufin yiwa yara 80,772 marasa allurar riga-kafi allura a ƙananan hukumomi bakwai waɗanda suka fi samun rashin yiwa yara rigakafi kafin Disamba 2027. An ƙaddamar da shirin, mai taken Z-TRACE: Bin diddigi a Zamfara da kuma daidaita allurar riga-kafi, a yau Laraba, a wani taron fara aiki na kwana ɗaya da aka gudanar a Karma Guest Inn, Gusau. Da yake gabatar da jawabin maraba, daraktan shirye-shirye na Gidauniyar Sultan Foundation, Aminu Inuwa Muhammad, ya ce Zamfara tana da kimanin…
Read More
Ranar Hausa ta duniya: Sarakuna da masana sun nemi kare harshen Hausa

Ranar Hausa ta duniya: Sarakuna da masana sun nemi kare harshen Hausa

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Manyan baƙi da masu ruwa da tsaki a harkar raya harshen Hausa sun jaddada muhimmancin kare harshen da al’adun Hausawa, tare da kira ga al’umma, musamman matasa, da su rungumi harshen domin tabbatar da ɗorewarsa a wannan zamani na fasahar sadarwa. Sun bayyana hakan ne a wajen bikin Ranar Hausa ta duniya, wanda ya haɗa manyan baƙi daga ciki da wajen Jihar Kano, ciki har da sarakuna, malamai, masana da shugabannin al’umma masu ruwa da tsaki wajen bunƙasa harshen Hausa da kare al’adun Hausawa. Da yake gabatar da jawabinsa, Mai Martaba Ambasada Alhaji Ibrahim Haruna,…
Read More
Ƙungiyoyi 100 a Zamfara na goyon bayan Tinubu da Gwamna Lawal su zarce

Ƙungiyoyi 100 a Zamfara na goyon bayan Tinubu da Gwamna Lawal su zarce

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Hukumar kula da harkokin siyasa ta Jihar Zamfara ta gudanar da taron wayar da kan jama'a na kwanaki biyu da kuma gangamin goyon bayan Gwamna Dauda Lawal da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a karo na biyu a shekarar 2027 a Zamfara. Bitar ta gudana yau Laraba a Gidan Alh. Umaru Shinkafi, Unguwar Gwaza, kusa da Hedikwatar 'yan sanda, Gusau. Da yake jawabi a lokacin taron, mai ba da shawara na musamman ga gwamna kan harkokin Siyasa, Hon. Alhaji Nura Sani Abdullahi, ya ce an tsara wannan gangamin ne don ƙarfafa nasarorin da Gwamna Lawal da…
Read More
Tamuwa: Red Cross ta tallafa wa gwamnatin Katsina da katan 700 na ƙwamaso

Tamuwa: Red Cross ta tallafa wa gwamnatin Katsina da katan 700 na ƙwamaso

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Jihar Katsina ta karɓi katan 700 na ɗan ƙwamaso (RUTF) daga Ƙungiyar Red Cross ta Najeriya, domin tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na yaƙi da tamowa, a tsakanin yara. An miƙa kayan ta hannun Kungiyar reshen Jihar Katsina. Za a rarraba ga yaran da ke fama da tamowa a faɗin jihar, tare da tabbatar da cewa kayan sun isa ga waɗanda aka tanada kuma an yi amfani da su yadda ya kamata. Wannan ba shi ne karon farko da Red Cross ke tallafa wa Katsina wajen yaƙi da tamowa ba. A irin wannan lokaci a shekarar…
Read More
Hausawa mutane ne masu son haɗin kai da ci gaban Najeriya – Tinubu

Hausawa mutane ne masu son haɗin kai da ci gaban Najeriya – Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce Hausawa na taka muhimmiyar rawa wajen haɗin kai da ci gaban Najeriya, tare da yaba wa gudunmawar da al'ummar ke bayarwa wajen bunƙasa ƙasar. Tinubu ya bayyana haka ne yayin da yake taya al'ummar Hausawa murnar ranar Hausa, wadda ake gudanarwa a masauratar Daura, da ke jihar Katsina cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X. Shugaba Tinubu ya ƙara da cewa harshen Hausa ya bunƙasa sosai, kuma ya zama wani muhimmin harshen sadarwa da kasuwanci a sassa daban-daban na duniya. Shugaban ya kuma taya ɗaukacin al'ummar Hausawa murna, yana mai…
Read More
Yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani: Tasirinsu, damarmaki da ƙalubale kashi na biyu

Yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani: Tasirinsu, damarmaki da ƙalubale kashi na biyu

Daga BILKISU YUSUF ALI, Ph’D Gabatarwa: Kamar yadda muka faro bayani a makon da ya gabata. Kafafen sadarwa na zamani sun zama ginshiƙin sadarwa a ƙarni na 21. Sun sauƙaƙa yaɗa bayanai da ilimi da  kasuwanci da  siyasa da hulɗar jama'a cikin sauri. Duk da haka, rashin amfani da su yadda ya kamata na iya haifar da yaɗuwar labaran ƙarya da zamba ta yanar gizo da cin zarafi da rashin tsaro. Wannan takarda ta yi bayani kan ma'anar kafafen sadarwa na zamani, nau'o'insu, yadda ake amfani da su cikin hikima, fa'idodinsu, ƙalubalen da suke tattare da su, da hanyoyin inganta…
Read More
Yaƙin Basasar Kano (1894–1895)

Yaƙin Basasar Kano (1894–1895)

Shekaru 131 kenan tun bayan da al'ummar Kano suka tsinci kansu cikin mummunan yaƙin basasa sakamakon rikicin sarauta tsakanin gidan Sarkin Kano Abdullahi Maje Karofi da gidan Sarkin Kano Muhammadu Bello, waɗanda dukkansu 'ya'yan Sarkin Kano Ibrahim Dabo ne. Masana tarihi sun bayyana wannan yaƙi a matsayin mafi muni da birnin Kano ya taɓa fuskanta. An rawaito cewa wani Bature da ya ziyarci Kano a lokacin ya ce, "Kano ta zama ƙasar jini saboda irin yawan jinin da aka zubar." Wannan yaƙi ya haifar da babbar asara ga rayuka, dukiyoyi da kuma tattalin arzikin birnin. Asalin rikicin: Bayan rasuwar Sarkin…
Read More