26
Aug
Daga UMAR GARBA a Katsina Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa Ibrahim Masari da gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, sun yi alƙawarin bayar da gudummawar Naira miliyan 600 domin gina Jami’ar Fortune da JIBWIS ke ginawa a Jihar Bauchi. Masari da Buni za su bayar da Naira miliyan 300 kowannensu. Sai dai gudummawar ta zo ne a lokacin da ake ta muhawara kan alaƙar siyasa da addini, musamman bayan Shugaban Majalisar Malamai na JIBWIS, Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir, ya fito fili yana goyon bayan Shugaba Tinubu da sake zaɓensa a 2027. Jaridar Daily Trust ta…
