
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Majalisar Zartarwar Jam’iyya mai mulki (APC) ta sanar da Ministan Jinƙai, Farfesa Nentawe Goshwe Yiltwatda a matsayin sabon shugabanta na Ƙasa.
Hakan ya faru ne makonni kaɗan da Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga muƙamin bisa wasu dalilai da aka alaƙanta da kiwon lafiyarsa.
Sauran bayanai za su biyo baya…
