Kotu ta tsayar da ranar gabatar da hujjoji a shari’ar Shinkafi da Sanatan APC na Zamfara ta Arewa

Spread the love

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau

Babbar Kotun Tarayya da ke a Gusau, Jihar Zamfara, ta tsayar da Talata, 5 ga Agusta, 2026, domin karɓar ƙarshen-hujjojin rubutu a shari’ar da jigo a jam’iyyar APC, Dr. Sani Abdullahi Shinkafi, ya shigar kan sakamakon zaɓen fidda gwani na Sanatan Zamfara ta Arewa.

Lauyan mai shigar da ƙara, Barr. Bello Galadi, ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan zaman kotun na yau Talata a harabar kotun da ke Gusau.

A cewar Galadi, an ɗage zaman ne saboda jam’iyyar All Progressives Congress (APC) wadda ita ce ta ɗaya a cikin waɗanda ake ƙara, ta gabatar da takardar amsa ga kiran da aka yi mata na zuwa kotu.

Ya ce tawagar lauyoyin sun yi amfani da sashe na 7 dokar 6 na jagoran Amayyuka na babbar kotun tarayya kan shari’o’in da suka shafi zaɓe kafin a gudanar da su. Wannan sashe yana ba mai shigar da ƙara damar kwana uku domin mayar da martani kan takardar amsar da wanda ake ƙara ya gabatar.

“Mun sanar da kotu cewa muna da damar gabatar da martaninmu game da takardar amsar da APC a matsayin ta ɗaya a cikin waɗanda ake ƙara ta gabatar cikin kwana uku a wannan shari’a,” in ji Barr. Galadi.

Dr. Shinkafi ya shigar da shari’ar mai lamba FHC/GS/CS/6/2026 a kan APC, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), da Sanata Sahabi Ya’u Kaura a matsayin na ɗaya, na biyu, da na uku a cikin waɗanda ake ƙara.

Yana ƙalubalantar cire sunansa da hana shi shiga zaɓen fidda gwani na APC da aka gudanar a ranar 19 ga Mayu, 2026, na mazaɓar Sanatan Zamfara ta Arewa.

A cikin shari’ar, Dr. Shinkafi na roƙon kotu ta tantance halaccin zaɓen fidda gwanin tare da soke tsarin da ya fitar da Sanata Sahabi Ya’u Kaura a matsayin ɗan takar APC na mazabar.

Shinkafi ya bayyana cewa zaɓen ya cika da rashin daidaito kuma bai bi dokar zaɓe ba, ƙa’idojin INEC, da kuma kundin tsarin mulki da jagororin zaɓe na APC kan yadda ake gudanar da zaɓen fidda gwani kai tsaye.

A zamanan da suka gabata, kotu ta saurari hujjoji kan buƙatun da aka gabatar kuma ta ba ɓangarorin damar gyara takardunsu.

Yanzu dai kotu ta tsayar da 5 ga Agusta domin gabatar da ƙarshen-hujjojin rubutu, lamarin yana kusa da yanke hukunci.

Barr. Galadi ya sake jaddada cewa wanda yake karewa Dr. Sani Abdullahi Shinkarfi bai gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwanin ba, kuma yana neman kotu ta shiga domin tabbatar da bin tsari da dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyar.

By ukarofi

Leave a Reply