Daga ABDULLAHI DANJUMA a Abuja
Shugaban Katampe, Mista Daniel Sarki ya naɗa Alhaji Aliyu Musa a matsayin Sarkin Sadauki Sabon Wuse.
An naɗa Sarkin Sadauki Sabon Wuse tare da wasu mutane 15, a wani biki mai ƙayatarwa da aka gudanar a Fadar Sarkin da ke Katampe, ƙaramar Hukumar Tafa ta jihar Neja a ƙarshen mako.
Yayin da yake naɗa Sarkin Sadauki Sabon Wuse da sauran waɗanda suka samu nasara, Sarkin ya ƙarfafa musu gwiwa da su yi amfani da rawar da suka taka wajen samar da zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaba a cikin Sabon Wuse, musamman a masarautar Suleja.
Ya bayyana cewa an naɗa su waɗannan muƙamai ne domin a yaba musu da kuma ƙarfafa musu gwiwarsu da kuma aiki tuƙuru wajen fafutukar zaman lafiya da ci gaba a yankin Sabon Wuse.
A wata liyafa da aka shirya domin naɗin nasu, Alhaji Aliyu Musa ya nuna matuƙar godiyarsa ga Allah Maɗaukakin Sarki da kuma Shugaban Katampe saboda ganin ya cancanci wannan sarauta ta Sarkin Sadauki, a cikin mutane da dama da suka cancanta a masarautar.
Ya sake nanata ƙudirinsa na inganta zaman lafiya da haɗin kai, kuma ya yi alƙawarin ci gaba da tallafawa shirye-shiryen da ke haifar da ci gaba mai ma’ana.
Sarkin Sadauki ya kuma shawarci mutane a ko’ina da su goyi bayan manufofin gwamnati da sauran hukumomi da aka kafa domin kawar da mummunan tasiri, musamman tsakanin matasa, da kuma gina al’umma mai adalci inda wadata da zaman lafiya suka bunƙasa.
Taron ya shaida ƙoƙarin Shugaban na karramawa da girmama mutanen da suka bayar da gudummawa mai yawa ga ci gaban Masarautar da kuma jihar bakiɗaya.
Masu jawabi daban-daban sun yaba wa Sarkin Sadauki da sabbin masu riƙe da sarautar saboda sadaukarwarsu da jajircewarsu ga ayyukan gwamnati, kuma an ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da aiki don inganta al’ummominsu.
