Yadda wata uwa ke lalata da ’ya’yanta a bidiyo don samun kuɗi ta intanet

Spread the love

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Anambra ta kama wata mata mai shekaru 36, Anulika Onyeanusia, bisa zargin yin lalata da ’ya’yanta tare da amfani da hotuna ko bidiyon da aka samu daga wannan mummunan aiki wajen neman kuɗi ta intanet.

Lamarin ya shiga hannun ’yan sanda ne bayan wani faifan bidiyo mai tayar da hankali ya bazu a kafafen sada zumunta, lamarin da ya sa rundunar ta fara gudanar da bincike.

Daga bisani, jami’an ’yan sandan sun gano inda matar take a Onitsha, inda suka kama ta tare da ceto yara huɗu da suke ƙarƙashin kulawarta.

Yaran, waɗanda shekarunsu ke tsakanin biyu zuwa tara, yanzu haka suna ƙarƙashin kariyar hukumomi yayin da masu bincike ke ƙoƙarin gano cikakken abin da ya faru da kuma tantance ko akwai wasu mutane da ke da hannu a lamarin.

Mai magana da yawun Rundunar ’Yan Sandan Jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da kama matar, yana cewa matakin ya biyo bayan bayanan sirri da rundunar ta samu daga wasu abubuwan da ke yawo a kafafen sada zumunta.

Rundunar ta ce, jami’anta sun kuma ƙwato wasu kayayyaki da ake ganin za su taimaka wajen gudanar da binciken daga wurin da aka kama matar.

Ana sa ran binciken zai gano tsawon lokacin da ake zargin cin zarafin ya gudana, irin yadda aka aikata shi, da kuma ko wasu mutane sun taimaka wajen samarwa ko yaɗa abubuwan da ake zargin an ɗora a intanet.

Bayanan farko da suka fito daga binciken sun nuna cewa ana zargin lamarin ya haɗa da yin amfani da ɗaya daga cikin yaran wajen samun kuɗi ta hanyar intanet.

Rahotanni sun ce matar ta amince wa masu bincike cewa ta samar da wasu hotuna ko bidiyo da suka shafi ’yarta mai shekaru takwas, sannan ta ɗora su a intanet.

An ruwaito cewa, ta shaida wa masu binciken cewa ta samu kuɗaɗen shiga daga yaɗa waɗannan abubuwa, inda wani rahoto ya ce kuɗin da ta samu ya kai kusan dala 300.

Zargin ya ƙara jawo hankalin jama’a kan barazanar da yara ke fuskanta daga manya da ke amfani da kafafen zamani wajen cin zarafinsu domin samun kuɗi.

Masu bincike na sa ran bin diddigin harkokin intanet da suka shafi abubuwan da ake zargin an yaɗa, domin gano inda aka ɗora su, wacanda suka samu damar shiga ko yaɗa su, da kuma ko matar ta samu taimakon wasu mutane.

Sai dai ’yan sanda ba su ce an kammala binciken ba, don haka zarge-zargen da ake yi wa matar na ci gaba da kasancewa ƙarƙashin bincike, kafin a yanke hukuncin ko za a gurfanar da ita a gaban kotu.

Kama matar ya kuma haifar da ceto yara huɗu masu shekaru biyu, uku, shida da tara.

Rundunar ta ce an kai yaran ƙarƙashin kulawar hukumomi domin kare lafiyarsu, yayin da ake ɗaukar matakan tabbatar da samun kulawa da kariyar da suka dace a lokacin da binciken ke ci gaba.

Ceton yaran ya sa masu bincike suka fara duba ko abin da ake zargin ya faru sau ɗaya ne kawai, ko kuma akwai yiwuwar ya kasance wani tsari da ya daɗe ana aiwatarwa.

Hukumomi za su yi hira da mutanen da suka dace tare da nazarin shaidun da ake da su, domin gano abin da ya faru da kowane ɗaya daga cikin yaran da kuma ko akwai wanda ya taɓa fuskantar cin zarafi.

Saboda lamarin ya shafi ƙananan yara, ba a bayyana sunayensu ba.

Masana harkokin kare haƙƙin yara sun daɗe suna jaddada muhimmancin kare waɗanda aka ci zarafinsu daga sake fallasa su, musamman a kafafen sada zumunta, inda hotuna ko bidiyon da suka shafe su za su iya ci gaba da yawo ko da bayan fara bincike.

’Yan sanda sun kuma yi wa mijin matar tambayoyi a wani ɓangare na binciken, domin gano ko yana da masaniya kan ayyukan da ake zargin matarsa da aikatawa.

Sai dai yin masa tambayoyi ba yana nufin an tabbatar da cewa yana da hannu a laifin ba. Masu bincike ne za su tantance ko yana da masaniya kan abin da ake zargin, ko kuma yana da wata alaƙa da samarwa ko yaɗa abubuwan da ake bincike a kansu.

Saboda haka, binciken na iya faɗaɗa zuwa wasu mutane idan aka gano wasu hujjoji da ke nuna cewa akwai ƙarin waɗanda ke da hannu a lamarin.

Haka kuma, masu bincike za su binciki na’urorin sadarwa da sauran kayayyakin da aka kwato yayin samamen, domin haɗa bayanai da gano yadda abubuwan da ake zargin suka faru.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Anambra, CP Nnanna Oji Ama, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Shugabancin rundunar ya kuma jaddada muhimmancin ci gaba da kare yaran da aka ceto yayin da ake gudanar da binciken.

Rundunar ta bayyana zarge-zargen da cewa ba za a amince da irin wannan hali ba, tana mai cewa za a binciki dukkanin abubuwan da suka shafi lamarin kafin ɗaukar matakan doka da suka dace.

Binciken ya zo ne a lokacin da ake ƙara nuna damuwa kan yadda ake amfani da kafafen intanet wajen cin zarafin ƙananan yara, musamman ganin yadda abubuwan da suka shafi cin zarafi za su iya yacuwa cikin sauri zuwa ga ɗimbin mutane.

Ga waɗanda aka ci zarafinsu, illar irin wannan abu ba ta tsaya kan lokacin da aka aikata shi kawai ba, domin hotuna ko bidiyonsu na iya ci gaba da yawo a intanet tare da ƙara jefa su cikin damuwa da cutarwa.

By ukarofi

Leave a Reply