Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Mata sun gudanar da zanga-zanga a tuɓe domin bayyana fushinsu kan matsalar rashin tsaro a yankin Akoko da ke Jihar Ondo.
Matan sun gudanar da zanga-zangar ne suna masu nuna damuwa bisa yawan kashe-kashe da garkuwa da mutane da kuma lalata gonaki a yankin.
Masu zanga-zangar waɗanda yawancinsu tsofaffi ne suna zargin makiyaya da hannu a kashe-kashe da kuma lalata gonaki.
Sun yi tattakin nasu a tuɓe ne bayan kashe wani manomi mai suna Sunday Ayeni a yayin wani rikicin tsakaninsa da wasu makiyaya a gonarsa.
A ƙarshen mako ne aka tsinci gawarsa bayan an yi ta neman shi, lamarin da ya sa manoma watsi da gonakinsu saboda tsoron abin da ke iya biyo baya.
A yayin taron tsaro da aka gudanar a fadarsa, Olubaka na Oka, Adebori Adeleye, ya ce masu zanga-zangar sun buƙaci a bi wa waɗanda aka kashe haƙƙinsu.
Mai magana da yawun matan, Misis Abigail Ojo, ta zargi makiyaya da yin fyaɗe ga wasu mata a gonakinsu da kuma lalata musu amfanin gona.
Ta ce abin da ya faru ya sa sun yi watsi da gonakinsu, kuma ba za su koma ba sai sun samu tabbacin tsaro.
Don haka ta roki jami’an tsaro su magance matsalar baki ɗaya.
A nasa jawabin, basaraken, Mista Adeleye, ya ce jami’an tsaro na ɗaukar matakan magance matsalar tsaron yankin.
