
Daga BELLO A. BABAJI
Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ba zai samu halartar taron ƙasashen masu tattalin arziƙi (Commonwealth Heads) ba da za a yi Samoa, kamar yadda aka tsara.
Ofishin shugaban ƙasa ya sanar hakan jim-kaɗan bayan wani abu ya yi karo da jirginsa a wani filin jiragen sama na New York da ke Amurka wanda hakan ya sa aka soke zuwan Shettima taron.
A saboda haka ne aka samar da wata tawaga ƙarƙashin jagorancin Ministan Kula da Muhalli, Balarabe Lawal wadda za ta wakilci Nijeriya a taron, kamar yadda wata sanarwa da Mai taimaka wa shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar ta nuna.
A ranar Lahadi da ta gabata ne Shettima ya bar Abuja don halartar taron a madadin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda a sanadiyyar fashewar wani yanki na gilashin jirgin ya sanya aka soke zuwansa taron.
An fara taron na wannan shekarar ne a ranar 21 ga watan Oktoba wanda kuma za a kammala a ranar Asabar, 26 ga wata.
Za a gudanar da zaɓen Sakatare-Janar na taro na gaba da kuma tattauna muhimman batutuwa da suka ƙasashen suka haɗu a kai don samun cigaba mai ɗorewa a yankunansu.
