NiMET ta yi hasashen ruwan sama da tsawa na kwana uku daga Lahadi

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Hukumar Kula da Yanayi ta Ƙasa (NiMET) ta yi hasashen samun ruwan sama da tsawa a Nijeriya daga ranar Lahadi zuwa Talata.

A saƙon hasashen yanayi da ta fitar a ranar Asabar, hukumar ta ce za a samu tsawa da ruwan sama a wasu yankunan jihohin Taraba da Adamawa dake Arewacin Nijeriya.

Haka kuma, a lokacin rana da dare akwai yiwuwar samuwar tsawa da ruwan sama a jihohin Katsina, Kano, Zamfara, Kaduna, Jigawa, Borno, Gombe da Bauchi.

NiMET ta ce, a yammaci kuma an yi hasashen samun tsawa da ruwan sama a yankunan Abuja, Neja, Nasarawa, Kwara, Kogi, Benue da Filato.

A kudancin Nijeriya kuwa, za a samu hadari da yayyafi a lokutan safiya da yammaci a jihohin Oyo, Ogun, Ondo, Ebonyi, Ekiti, Edo, Abia, Imo, Enugu, Anambra, Legas, Akwa-Ibom, Kuros-Riba, Ribas, Delta da Bayelsa.

Har’ilayau, ta bayyana cewa za a samu tsawa a safiyar ranar Litinin a Sakkwato, Zamfara da Bauchi.

Bugu da ƙari, za a yi ruwa da tsawa a yankunan Sakkwato, Zamfara, Taraba, Adamawa, Katsina, Kano, Jigawa, Borno, Bauchi and Kaduna a yammaci.

By Babaji