An buƙaci a gudanar da bincike kan zargin sojoji da kisan mata a Adamawa

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

A jihar Adamawa, dubban jama’a daga Lamurde da makwabtan yankuna sun halarci jana’izar mata tara da ake zargin jami’an Sojojin Nijeriya sun kashe a yammacin Litinin.

An gudanar da jana’izar ne a filin ofishin ƙaramar hukumar Lamurde, inda ya zama wurin jimami da kuma kira ga gwamnati ta tabbatar da adalci.

An bayyana sunayen matan da suka riga mu gidan gaskiya, abin da ya ƙara hura wutar kira da alhini a tsakanin al’umma.

Bisa bayanai da jaridar SaharaReporters ta bayar, waɗanda suka mutu su ne: Florence Frank, Suzy Tanko, Marry Talmon, Mercy Kennedy, Lucky Yakubu, Pwamwasari Tami, Mary Shikauno, Destiny Gibson, da Hunbokwama Nickson.

An naɗe gawarwakin da farin zani da tabarma, aka jero su a layi ɗaya — abin da ya tunzura zukatan jama’a da suka zo kallo da kuka.

ƙungiyar matasan Bachama ta bayyana cewa sojoji ne suka buɗe wuta kai tsaye kan matan da ba su da wani makami ko barazana.

Sakatare Janar na ƙungiyar, Abner Kwakano, ya ce al’umma da idanuwansu suka shaida abin da ya faru, kuma akwai waɗanda suka tsira da jikkata a irin harbin nan.

Ya ce, “Mu muna nan akan magana ɗaya: sojoji ne suka harbe mata marasa laifi. Wannan gaskiya ce da al’umma suka gani. Ba za mu amince da wani danne bayanai ko karkatar da gaskiya ba.”

Kwakano ya kuma buƙaci a kafa kwamitin bincike mai zaman kansa, wanda ba zai karkata ga ɓangaren gwamnati ba, domin tabbatar da bin diddikin abin da ya faru da hukunta duk wanda aka samu da laifi.

Sai dai wata ƙungiya ta matasa daga ɓangaren Chobo ta ƙaryata rahotannin da ke alaƙanta rikicin da matasanta.

A wata sanarwa da sakatare Janar ɗin ƙungiyar, Injiniya Gideon Sam, ya fitar, ya ce Chobo ce ma ta fara fuskantar harin da ya laƙume gidaje da ƙauyuka, tare da mayar da alhakin rikicin ga wani ɓangaren Bachama.

ƙungiyar ta bayyana irin rahotannin da ke nuna cewa Chobo ce ta tayar da fitina a matsayin “abubuwan da ba su dace ba, sakamakon yaɗa labaran ƙarya da barazana ga zaman lafiyar yankin.”

Al’amarin ya ƙara tayar da ƙuda saboda tarihin zargin keta haddin bil’adama da ake yi wa Sojojin Nijeriya a lokuta daban-daban, ciki har da irin zargin kisan ’Yan Shi’a a shekarun baya — zargi da sojojin suka sha musantawa.

Yanzu dai idanuwa na kan gwamnatin tarayya da rundunar soji domin ganin an sami cikakken bincike, ba wai kawai don tabbatar da gaskiya ba, har ma don wanke sunan dukkan ɓangarorin da ba su da hannu da kuma tabbatar da adalci ga matan da suka mutu ba tare da kai musu agaji ba.

By ukarofi