Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Tunji Disu a matsayin muƙaddashin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, bayan amincewa da murabus ɗin Kayode Egbetokun – matakin da ke nuni da wani sabon salo a jagorancin harkokin tsaron cikin gida na ƙasa.
A hukumance, an bayyana cewa Egbetokun ya miƙa takardar murabus dinsa ne bisa dalilan iyali.
Mai bai wa Shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya ce Shugaba Tinubu ya nuna godiya ga tsohon Sufeto Janar ɗin bisa dogon aikin da ya yi wa rundunar ‘yan sanda da ƙasa baki ɗaya, yana yaba masa da jajircewa da ƙwarewa.
Sai dai wasu majiyoyi daga Fadar Shugaban ƙasa sun nuna cewa sauyin na iya wuce dalilan da aka bayyana a takarda.
Rahotanni sun ce an daɗe ana samun saɓanin fahimta kan alƙiblar gyaran harkokin tsaro, musamman dangane da ƙudurin kafa ‘yan sandan jihohi – wani tsari da Shugaba Tinubu ya daɗe yana fafutukar aiwatarwa domin tinkarar matsalolin tsaro da suka mamaye jihohi daban-daban.
An ruwaito cewa an gudanar da taruka a Majalisar Tattalin Arziki ta ƙasa domin hanzarta shirye-shiryen dokoki da tsarin aiwatar da ‘yan sandan jihohi. Amma wasu na ganin cewa jagorancin rundunar a wancan lokaci bai nuna cikakken goyon baya ko saurin aiwatar da wannan manufa ba, lamarin da ya haifar da rashin jituwa a wasu muhimman matakai na gwamnati.
Bugu da ƙari, taɓarɓarewar tsaro a wasu sassan Arewa ta ƙara jefa matsin lamba kan gwamnatin tarayya. Rahotanni sun nuna cewa a watan Fabrairun 2026 kadai, rayuka kusan 800 sun salwanta sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a yankunan noma. A jihar Taraba, hare-hare a ƙananan hukumomin Takum da Donga sun haddasa asarar rayuka da dama, lamarin da ya sa gwamnan jihar, Agbu Kefas, ya gana da Shugaba Tinubu domin tattauna matsalar.
Ko da yake ba a fitar da cikakken bayanin tattaunawar ba, majiyoyi na ganin cewa rikicin tsaro a Taraba da sauran jihohi ya ƙara fito da buƙatar sauyin dabaru da kuma hanzarta gyare-gyaren da gwamnati ke son aiwatarwa.
Naɗin Disu a matsayin muƙaddashin Sufeto Janar na ’Yan Sanda na zuwa ne a daidai lokacin da ake buƙatar sabbin dabaru da kuzari wajen fuskantar ƙalubalen tsaro. Masana harkokin tsaro na ganin cewa an san Disu da mayar da hankali kan ayyukan fili da kuma ra’ayin gyara, siffofi da za su iya dacewa da sabon salon da gwamnatin Tinubu ke son ganin an aiwatar cikin gaggawa.
A mahangar siyasa da tsaro, sauyin na iya zama wata alama ta shiga sabon babi – inda ake sa ran ƙarin ƙarfi, sauri da tsari a yunƙurin sake fasalin tsarin tsaron cikin gida na Nijeriya.
