
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Gwamnatin Tarayya ta fitar da lambobin waya na kiran gaggawa ga ‘yan Nijeriya da ke zama a ƙasashen yankin Gabas ta Tsakiya sakamakon ƙaruwa da rikicin yankin ke yi, wanda ya janyo fargaba ga lafiyar ‘yan ƙasa.
Ma’aikatar Harkokin Waje ta bayyana haka a wata takarda domin taimaka wa ‘yan ƙasa su samu tuntuɓa cikin gaggawa idan buƙatar hakan ta taso.
Ga cikakken jerin lambobin gaggawa da gwamnatin ta bayar:
Iran: +989393216872, +989024165493
Israel: +972543340414, +972503673175
Jordan: +962795669949, +962799430414
Lebanon: +96181669403, +96170848080
Qatar: +97466802029, +97450733786
Saudi Arabia: +966503862894, +966532198524
United Arab Emirates: +971504252546, +971503761332
An kuma umurci ‘yan Nijeriya da su ajiye waɗannan lambobin a wayoyinsu na hannu kuma su riƙa shafar ofisoshin jakadanci da konsule da sun bukaci taimako na gaggawa.
Kazalika, an shawarce su da su bi duk shawarwarin tsaro na hukumomin ƙasashen da suke ciki domin kare lafiyarsu yayin da rikicin ke cigaba da ta’azzara.
