
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Al’umma, Mohammed Idris Malagi, ya ƙalubalanci kira akan a dawo da tallafin fetur da aka cire a baya, yana mai gargaɗin koma wa tsarin na da ka iya haifar da cikas ga bunƙasar da aka samu a ɓangaren wadatar kuɗi, karya ƙwarin-gwiwar masu zuba jari da rushe nasarorin da aka samu sakamakon gyare-gyaren fannin tattali a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.
Shugaba Bola Tinubu dai ya cire tallafin fetur ne yayin da ya kama aiki a matsayin shugaban Nijeriya a watan Mayun 2023, matakin da ya zama ɗaya daga cikin ababen da suka haddasa matsi da cece-kuce a ƙarƙashin gyare-gyaren da gwamnatin nasa take yi wa harkar tattali.
Da yake tsokaci kan wata maƙala da aka wallafa a ranar 24 ga Agusta, 2026 a wasu jaridun ƙasa mai taken, “Restoring Fuel Subsidy Will Reverse Nigeria’s Economic Gains,” Minista Idris ya zayyano amfani na wadatar kuɗaɗe, haɗarin tattali da aka nesanta da kuma matsalolin da wahalar da ƙasar za ta samu kanta aciki muddin aka dawo da tallafin fetur.
Ya ce, masu neman a dawo da tallafi wajibi ne su shirya fuskantar abin da ya kira da ainihin ƙalubalensa musamman wajen buƙatar gogayya kan albarkatun gwamnati a lokacin da Nijeriya take ƙoƙarin neman hanyoyin da za ta bi wajen ƙarfafa matakin samun wadataccen kuɗi a muhimman fannonin tattalin arziƙinta.
Ya tunatar da cewa, a shekarar 2022 yayin da ake tsaka da halin gazawar samar da wadataccen mai da ƙarancin kuɗin shiga, Nijeriya ta kashe sama da Dala biliyan 10 a tallafin fetur, yayin da Babban Bankin Duniya ya yi gargaɗin cewa tallafi na zuƙe arziƙi da da zai tallafa wa ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa da kariyar zamantakewa.
Mohammed Idris ya ƙara da cewa, an tara jimillar Naira tiriliyan 15.8 ga asusun ƙasa a tsakanin Yunin 2023 da kuma Disambar 2025, kamar yadda Ministan Kuɗi da Harkokin Tattali, Dakta Taiwo Oyedele ya bayyana yayin gabatar da amfanin da aka samu a sanadiyyar cire tallafin fetur.
Ya bayyana cewa, jimillar tiriliyan N5.43 ne ya shiga asusun gwamnatin tarayya, tiriliyan N6.52 ga jihohi da kuma Naira tiriliyan N3.88 ga ƙananan hukumomi, yana mai cewa hakan na wakiltar matakin wadatar kuɗi da aka samu da kuma yadda aka sarrafa su a faɗin ƙasar.
Har ila yau, ya ce ƙarin kuɗin shiga da gwamnati ta samu kan matakin ya taimaka mata wajen ƙarfafa wa jihohi da ƙananan hukumomi ta yadda suke iya biyan kuɗaɗen albashi da fansho ba tare da takura ba da kuma tallafa wa muhimman harkokin gwamnatin tarayya da suka haɗa da aiwatar da ababen more rayuwa, tsaro, noma da ci-gaban harkar inganta ɗan-adam.
