
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
An sace wani ɗan Chana bayan kashe jami’an Hukumar Cibil Defens (NSCDC) su guda takwas a yankin Okpella da ke Ƙaramar Hukumar Etsako ta Kudu a Jihar Edo.
Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun kuma raunata wasu jami’an NSCDCn guda huɗu da wani farin hula, waɗanda suke karɓar a wani asibiti.
Lamarin ya auku ne a lokacin da jami’an hukumar da aka tura aiki a kamfanin siminti na BUA da ke jihar ke rakiyar wasu ƴan Chana biyar bayan dawowa daga sintiri, a bakin shiga farfajiyar kamfanin.
Majiyoyi sun shaida wa manema labarai cewa ƴan bindiga sun kai wa tawagar jami’an farmaki ne ɗauke da wasu muggan makamai inda suka halaka guda takwas a nan take.
NSCDC ta tabbatar da aukuwar lamarin a wata takarda ranar Asabar.
Ta bayyana cewa, al’amarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na dare a ranar Juma’a, 5 ga watan Satumba, 2025.
Tuni aka garzaya da gawawwakin mamatan wajen ajiyar gawawwaki yayin da kuma ake bai wa waɗanda suka jikkata magani.
