Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD
An bayyana cewa, har yanzu Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Neja ba su cika alƙawuran da suka yi wa waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a Mokwa ba kusan watanni biyar bayan afkuwar iftila’in.
Malam Zubairu Abdullah Anas, tsohon sakataren yaɗa labarai na kwamitin tallaf wa waɗanda abin ya shafa, ne ya bayyana haka yayin tattaunawa da Crusaders Radio, wata kafar intanet da ke Minna, ranar Asabar.
A lokacin da ambaliyar ta faru, Gwamna Umaru Bago ya yi alƙawarin sake gina gadar Mokwa-Rabbah da kuma biyan naira miliyan ɗaya ga kowanne mutum da ambaliyar ta shafa, domin samun wuri na wucin gadi kafin gwamnatin tarayya ta sake gina yankin. Haka kuma, gwamnatin tarayya ta yi alƙawarin gina yankin da ambaliyar ta lalata.
Sai dai a cewar Anas, waɗannan alƙawura sun tsaya ne kawai a magana.
“Mutanen da abin ya shafa ba su samu komai gaba ɗaya ba. Daga cikin kuɗin tallafi, hatsi, da kuma batun sake gina yankin — ba kowa ne ya samu ba,” inji shi.
Ya ƙara da cewa, “Ina iya cewa kusan kashi 55 cikin 100 ne kacal suka karɓi kuɗi, yayin da kashi 45 suka samu hatsi. An ware wurin da za a sake gina yankin, amma babu wani abin da ke gudana a wajen. Sama da watanni biyar kenan, amma babu wani aiki. Muna so mu ga aiki kafin mu yarda cewa gwamnati ba ta manta da waɗannan mutane ba.”
Anas ya bayyana cewa waɗanda suka samu kuɗi sun samu damar hayar gida, amma sauran da ba su samu ba suna yawo suna neman mafaka wajen ’yan uwa.
“Da ba saboda gwamnatin jiha ta rufe sansanin ba, da har yanzu mutane suna can suna kwana. Yanzu kuwa muna karɓar kira iri-iri daga mutane suna zarginmu da cewa mun ci kuɗinsu, alhali mu babu abin da muka karɓa. Kuɗin ma har yanzu suna hannun gwamnati.”
Ya ce, su kan ci gaba da roƙon gwamnati ta biya alƙawarinta, domin mutanen suna nuna ɓacin rai sosai.
“Kwanan nan mun yi taro da su, suna barazanar yin zanga-zanga. Mun sanar da su cewa an miƙa sunayen waɗanda abin ya shafa zuwa ga gwamnatin jiha domin sake tantance su. Haka ma waɗanda suka mutu — magadansu har yanzu ba su samu ko sisi ba.”
Anas ya bayyana damuwarsa da yadda lamuran ke tafiya, yana mai cewa, “Da gaske ne, abin yana nuna kamar gwamna ba ya da niyyar biyan kuɗin. Idan da yana son biyan, ba zai gagara ware miliyan 50 ko 100 ko 200 ba don wannan aiki.”
A yanzu dai, mutanen Mokwa da ambaliyar ruwa ta raba da muhallansu suna ci gaba da neman taimako da kulawa daga hukumomi, yayin da babu wani aikin sake gina yankin da aka fara a fili.
