Hukumar Alhazai ta Jigawa ta maida wa maniyyata 609 da kuɗaɗensu

Spread the love

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta maida wa maniyyata 609 waɗanda suka biya kuɗaɗe don Hajjin 2020/2921 da kuɗaɗensu har Naira miliyan 752.

Sakataren hukumar, Alhaji Muhammad Sani Alhassan, shi ne ya bayyana haka a Asabar da ta gabata yayin zantawarsu da manema labarai a garin Dutse, babban birnin jihar.

Alhassan ya ce, Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON), ita ce ta ba da umarnin da a gaggauta maida wa maniyyatan da kuɗaɗensu bayan da ƙasar Saudiyya ta bayar da sanarwar hana maniyyatan wasu ƙasashen duniya zuwa aikin Hajji a matsayin wani mataki na yaƙi da yaɗuwar cutar korona.

Alhassan ya bayyana cewa maniyyata 1,165 suka biya kuɗaɗensu don Hajjin 2020/2021.

Ya ce, “Daga cikin maniyyata 1,165, an maida wa mutum 609 da kudaɗensu yayin da maniyyata 556 suka zaɓi a ci gaba da riƙe nasu kuɗin don Hajji mai zuwa.”

Haka nan, ya ce yayin shirye-shiryen aikin Hajji na gaba za a ba da fifiko ga maniyyata 556 da ba su karɓi kuɗaɗensu ba.

A ƙarshe, Alhassan ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da yin addu’ar zaman lafiya da samun daidaito ga ƙasa da kuma fatan ganin karshen annobar korona.

By Editor