Isra’ila ta dakatar da jiragen agaji zuwa Gaza

Spread the love

A ranar 2 ga Oktoba, 2025, rundunar sojin ruwa ta Isra’ila ta dakatar da jiragen ruwa 13 daga flotilla mai ɗauke da kayayyakin agaji da ‘yan rajin kare hakkin jama’a, waɗanda suka nufi Gaza. Flotilla ɗin, mai suna Global Sumud, ta ƙunshi kusan jirage 40 kuma ta ɗauke fiye da mutane 500 daga ƙasashe da dama. 

Wani bidiyo da sojojin Isra’ila suka fitar ya nuna yadda aka sha ruwa da harsashi ruwa (water cannons) ga ɗaya daga cikin jiragen, yayin da aka kama Greta Thunberg tare da wasu daga cikin masu rajin. Isra’ila ta bayyanawa duniya cewa jiragen sun kusanci wani yanki mai aiki na soja, kuma ta ce akwai bayanan da suka nuna cewa ana ɗauke da kayayyakin harbi a wasu jiragen. 

Amma shugabannin flotilla sun musanta zargin Isra’ila, sun ce kamun an yi shi a cikin tekun duniya international waters, wanda zai saba da dokar kasa da kasa. Sun ce an katse sadarwa, an toshe sigina, an kuma hana watsa labarai domin hana duniya ganin abin da ke faruwa. 

A halin yanzu, jiragen da ba a dakatar ba sun kasance a kusan 46 nautical miles daga gabar Gaza, amma suna fuskantar tashin hankali daga sojojin ruwa da na sama. 

Masana diflomasiyya sun ce wannan lamari ya nuna yadda Isra’ila ke amfani da dalilan tsaro wajen toshe wadatar agaji. Duk da haka, kotunan duniya da ƙungiyoyin kare hakkin bil’adama sun yi gargaɗin cewa hana jiragen da ke ɗauke da agaji, musamman idan ba su nuna makamai ba, na iya zama ƙeta dokokin kasa da kasa.

ƙasashen Turai, musamman Italiya da Turkiyya, sun yi tir da matakin. A Italiya, an gudanar da zanga-zanga da yajin aiki a matsayin martani. Wannan na iya matsa wa EU da ƙasashe su ɗauki matakai na takunkumi ko shigar da ƙararraki a Majalisar ɗinkin Duniya.

Yayin da Gaza ke fama da matsalolin abinci, magunguna, ruwa da wutar lantarki, wannan mataki na dakatar da agaji zai ƙara wahala ga fararen hula. Masu aikin agaji sun yi gargaɗin cewa mutuwar jama’a za ta ƙaru idan irin wannan toshewa ta ci gaba.

Masana doka sun ce al’amuran kamar toshe jiragen a cikin teku, katse sadarwa, dakatar da kayayyaki duk suna buƙatar bincike mai zurfi. An ruwaito cewa flotilla za ta ƙara ƙarfafa matakan su, har zuwa ƙoƙarin bunkasa hanyoyin sadarwa daban-daban da kirkirar hanyoyi na daban domin tsallake toshewar.

Wannan mataki na iya jawo karin martani daga Hamas da ƙungiyoyi masu alaƙa, wanda zai iya tsananta harin da mayar da martani.

By ukarofi