Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ganawarsa da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ba ta haifar da wata yarjejeniya tabbatacciya ba dangane da batun Iran, sai dai an amince da ci gaba da tattaunawa.
Wannan shi ne karo na bakwai da shugabannin biyu suka gana cikin watanni 13 da suka gabata.
Trump ya jaddada cewa, duk wata yarjejeniya dole ta tabbatar da cewa Iran ba za ta mallaki makamin nukiliya ko makamai masu linzami ba. Isra’ila na son tattaunawar ta wuce batun nukiliya kadai ta hada da makaman ballistic da kuma goyon bayan ƙungiyoyin da take ɗauka a matsayin barazana.
Iran ta ce shirinta na nukiliya na zaman lafiya ne, kuma ba za ta tattauna batun makamai masu linzami ba.
An kuma tattauna batun Gaza da yarjejeniyar tsagaita wuta. Duk da cewa an samu wasu ci gaba, har yanzu akwai giɓin fahimta kan makomar makaman Hamas da kuma janye sojojin Isra’ila.
Masu sharhi na ganin cewa yankin Gabas ta Tsakiya na fuskantar wani yanayi mai sarkakiya, inda kowanne kuskure ka iya tayar da sabuwar gobara.
