Wike ya ƙwace takardun filaye 485 a Abuja ciki har da na Cocin Redeemed da Ma’aikatar Shari’a

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya amince da soke takardun filaye guda 485 a Abuja sakamakon rashin bin hanyoyi da doka ta tanada na tantance su daga hukumomin gwamnati.

An soke takardun ne bayan nazari akansu da sashen kula da lamuran filaye da haɗin-gwiwar ofishin tsare-tsaren filayen Abuja suka gudanar.

A cewar jami’ai, an gano cewa takardun ba a tabbatar da su akan abin da ya shafi tantancewa ba, lamarin da ya sa da dama aka tabbatar da su a matsayin ‘yan jabu.

Tuni dai a wata takardar sanarwar al’umma aka tabbatar da cire waɗanda aka tabbatar na jabu ne daga sahun masu neman a tabbatar da su a hukumance, musamman waɗanda suka miƙa buƙatarsu daga takardun ƙananan hukumomi domin tantancewa.

Sokewar ta shafi yankuna kamar haka; Ushafa Village Expansion Scheme, Ushafa Extension da kuma Dawaki Extension 1 a Ƙaramar Hukumar Bwari .

Sai kuma Ƙaramar Hukumar Birni (AMAC), inda ya shafi yankunan Kurudu-Jikwoyi Relocation, Kurudu Commercial, Karu Village Extension, Nyanya Phase IV Extension, Jikwoyi Residential, Sabon Lugbe da kuma Lugbe I Extension.

Haka ma Kuchiyako One layout a Ƙaramar Hukumar Kuje, inda nan ma dokar ta shafi cocin Redeemed da Ma’aikatar Shari’a da kuma Staff Multi-purpose Cooperative Society da dai sauransu.

By Babaji