Yadda ‘yan bindiga suka sace ɗalibai 8 a Kaduna

Spread the love

Daga WAKILINMU

Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar cewar an sace wasu ɗaliban jihar su takwas tare da wasu mazauna yankin.

Gwamnatin ta ce ɗaliban da lamarin ya shafa ba a harabar makaranta aka sace su ba.

A ranar Litinin ‘yan bindiga suka sace mutum 10 a Sakandaren Gwamnati da ke Awon a yankin Ƙaramar Hukumar Kachia a jihar.

Wannan shi ne hari na baya-bayan da ‘yan bindiga suka kai a jihar duk da ƙoƙarin da gwamnatin jihar tare da hukumomin tsaro ke yi wajen daƙile matsalar tsaro a faɗin jihar.

Gwamnatin jihar ta bakin Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida na jihar, Samuel Aruwan, ta ce ta gano ɗaliban da lamarin ya shafa ba a cikin makaranta aka yi garkuwa da su ba.

Ta ce hakan ya auku ne a lokacin da ɗaliban ke kan hanyarsu ta komawa gida inda ‘yan bindigar suka sace su tare da wausu mutane.

Tuni dai Gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, ya yi tir da lamarin tare da bayyana shi a matsayin abin takaici.

Gwamnan ya ce ya samu bayyanai kan tabbacin za a ceto ɗaliban su takwas da sauran waɗanda lamarin ya shafa nan ba da daɗewa ba.

By Editor