‘Yan sandan Afirka ta Kudu sun tabbatar da gano gawarwakin mata bakwai a kusa da Johannesburg

Spread the love

Daga AISHA ASAS

Rundunar ‘yan sandan Afirka ta Kudu ta kaddamar da bincike kan mutuwar mata bakwai da aka gano gawarwakinsu a yankin Ekurhuleni, gabashin birnin Johannesburg, cikin watanni biyu da suka gabata, lamarin da ya sake jefa jama’a cikin fargaba kan tsaron mata a kasar.

Rahotanni sun ce wasu daga cikin matan an same su ba tare da tufafi ba ko kuma da kadan daga cikin tufafinsu, yayin da wasu gawarwakin ke dauke da alamomin cin zarafin mata. Mafi yawancin wadanda abin ya shafi mata ne ‘yan shekaru 20 zuwa 30, yayin da daya daga cikinsu ta kasance matar da ta bace bayan ta fita daga gida domin yin gudu da rana.

Shugaban kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya bukaci hukumomin tsaro su zurfafa binciken lamarin, tare da alkawarin cewa ba za a bar wani abu da zai taimaka wajen gano gaskiyar abin da ya faru ba. Ya kuma bukaci a gano wadanda ke da hannu a kisan tare da gurfanar da su a gaban shari’a.

A halin yanzu, ‘yan sanda ba su tabbatar da cewa kisan matan yana da alaka da mutum guda ba. Suna binciken yiwuwar mutum daya ne ya aikata laifukan, ko kuma akwai wasu mutane da dama, ko kuma wasu masu aikata laifuka suka kwaikwayi irin wadannan hare-haren. Haka kuma, har yanzu ba a gano ainihin dalilin da ya sa aka kashe matan ba.

By ukarofi

Leave a Reply