Yan ta’adda sun saka bom ƙasan wata gada a Neja

Spread the love

Daga USMAN KAROFI

Aƙalla mutane takwas ne suka rasa rayukansu yayin da ake zargin wasu ‘yan ta’adda da suka sanya bama-bamai a kan wata gada mai muhimmanci da ke haɗa ƙauyukan Wawa da Luma a ƙaramar hukumar Borgu, Jihar Neja. Wannan harin ya faru ne da safiyar Litinin, inda gadar ta lalace, lamarin da ya shafi zirga-zirgar mazauna da ‘yan kasuwa, musamman waɗanda ke zuwa kasuwar iyaka ta Babana da ake yi kowace Litinin.

Rahotanni sun bayyana cewa mutanen da suka rasa rayukansu suna cikin motar da ke tafiye-tafiye tsakanin Nuku da Woro lokacin da ta taka bam ɗin, abin da ya janyo fashewar da ta kashe fasinjoji bakwai da direban motar baki ɗaya. Ana ganin wannan harin wani ɓangare ne na yunƙurin masu aikata laifin don hana gudanar da ayyukan tsaro a yankin.

SP Wasiu Abiodun, kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Neja, ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya ce ‘yan ta’addan da ake zargin suna aiki ne daga cikin Gandun Ƙasa na Kainji, inda suka yi amfani da bama-bamai wajen tarwatsa gadar. Ya ƙara da cewa, “Ana ci gaba da sa ido yayin da aka ƙara ƙarfafa ayyukan tsabtace yankin daga barazanar waɗannan masu laifi.”

Haka kuma, an samu rahotannin fashe-fashe a wasu wurare tsakanin Rafingiwa da Babana, da kuma a Woro da Kaiama, wanda ya tilasta wa mazauna guduwa. Har yanzu ba a tabbatar da ko akwai wasu waɗanda suka jikkata ba a waɗannan harin na biyu, yayin da hukumomi ke ci gaba da gudanar da bincike.

By ukarofi