ICPC za ta gurfanar da El-Rufai gaban kotu ranar Talata

Spread the love

Daga USMAN KAROFI

Hukumar yaki da rashawa da sauran laifukan da suka shafi rashawa mai zaman kanta (ICPC) ta sanar cewa za ta kawo tsohon Gwamna Nasir El-Rufa’i gaban kotu a ranar Talata mai zuwa a Kaduna.

Rahotanni sun nuna cewa El-Rufai yana tsare tun bayan ya amsa kiran hukumar EFCC a ranar 16 ga Fabrairu, 2026, inda aka yi masa tambayoyi na tsawon awanni 48 kafin ICPC ta ɗauke shi hannunta.

Tsawaita zaman tsarewar El-Rufai ya haifar da cece-kuce, inda ƙungiyoyi da mutane da dama suka buƙaci a gurfanar da shi a gaban kotu ko a sake shi. Kakakin ICPC, John Okor Odey, ya bayyana cewa El-Rufai zai fuskanci shari’a a kotun ƙoli ta tarayya da ke Kaduna a ranar Talata, ƙarƙashin lambar shari’a FHC/KD/73/2026, wanda ke da tuhuma da suka haɗa da satar dukiyar jama’a da kuma wanke kuɗaɗe.

Haka kuma, wata shari’a daban da aka ɗauki lamba KDH/KAD/ICPC/01/26, wanda ICPC ta shigar a Kotun Ƙoli ta Jihar Kaduna, ya haɗa El-Rufai da Malam Amadu Sule (LEDA), inda ake zarginsu da cin zarafi a ofis, damfara, niyyar yin damfara, da ba da fifiko ba bisa ƙa’ida. ICPC ta shigar da dukkan tuhumar a ranar 18 ga Maris, 2026, yayin da ranar gurfanarwa a kotun jihar za a sanar da ita daga baya.

By ukarofi