Yara miliyan uku za a yi wa rigakafin shan’inna a Katsina

Spread the love

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina

Za a yi wa yara aƙalla sama da miliyan uku allurar rigakafin cutar shan’inna a Jihar Katsina.

Babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko ta jihar, Dr Shamsudeen Yahaya, ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai a Katsina.

Ya ce allurar zai shafi yara ‘yan shekara huɗu a cikin matsugunai 19,790 a jihar.

Ya bayyana cewa an shirya gudanar da gangamin ne daga ranar 28 ga Maris zuwa 2 ga Afrilu, tare da ƙarin aikin gyaran fuska na kwanaki biyu kafin a kammala shi.

Ya ƙara da cewa sama da ma’aikata 10,000 za su shiga cikin aikin, ciki har da ma’aikatan da gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu.

A cewarsa Dr Shamsuddeen, abokan hulɗa kamar hukumar lafiya ta duniya da asusun yara na Majalisar Ɗinkin Duniya za su tura ma’aikata don tallafawa shirin.

“Jihohi da dama za su gudanar da shirin wayar da kan jama’a kan allurar riga-kafi a wannan lokacin, ciki har da Kwara, Niger, Kaduna, Kano, Jigawa, Bauchi, Yobe, Gombe, Adamawa, da Nasarawa,” in ji shi.

Dr Yahaya ya bayyana cewa an yi wa yara kimanin miliyan 2.6 allurar riga-kafi a lokacin atisayen bara, yana mai nuna fatan cewa kamfen na wannan shekarar zai cimma burin miliyan uku.

Ya ƙara da cewa duk da cewa jihar ta sami kimanin mutane biyu da suka kamu da cutar a ƙaramar hukumar Ɗanmusa, kamfen na yanzu yana da nufin tabbatar da cewa babu wanda ya kamu da cutar a nan gaba.

Ya yi kira ga jami’an yaɗa labarai da sauran masu ruwa da tsaki da su ƙara himma wajen wayar da kan jama’a don tabbatar da cewa an samu cimma nasarar wannan atisayen sosai.

By ukarofi