Za a samu tsayayyen lantarki a Nijeriya daga 2027 – Gwamnati

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jajirce wajen samar da tsayayyen wutar lantarki kafin ƙarshen gwamnatin sa a shekarar 2027.

Da yake magana a ranar Lahadin da ta gabata yayin ƙaddamar da tashar lantarki mai ƙarfin kilowatts 1ɗ15MɓA 33/11Kɓ a yankin Ikotun-Egbe a jihar Legas, Adelabu ya bayyana cewa ana samun gagarumin ci gaba a ƙarƙashin shirin ‘Renewed Hope’ na sake fasalin fannin samar da wutar lantarki a Nujeriya tare da kawo ƙarshen matsalar samar da wutar lantarki.

“’Yan Nijeriya za su iya tabbatar da aniyar shugaban ƙasa na ganin ‘yan ƙasar sun ci gajiyar wutar lantarki da ba ta katsewa kafin ya bar mulki,” inji Ministan.

Adelabu ya jaddada cewa, Gwamnatin Tarayya na bin matakai da dama don magance ƙalubalen da aka daɗe ana fama da shi a fannin lantarki, kuma duk da cika alƙawarin ba zai iya faruwa a cikin shekaru huɗu ba, burin 2027 na nan gaba.

A lokacin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Tinubu ya yi alƙawarin samar da ingantaccen lantarki cikin shekaru huɗu – alƙawarin da mutane da yawa ke ganin yana da buri idan aka yi la’akari da sarƙaƙiyar matsalar wutar lantarki a Nijeriya. Tun a wancan lokaci wannan alƙawari ya fuskanci idon jama’a, musamman ganin yadda rabin wa’adin mulkinsa ke gabatowa tare da ci gaba da taɓarbarewar ayyukan yi a sassan ƙasar da dama.

Kwanan nan, Bolaji Abdullahi, sakataren yaɗa labarai na riƙon ƙwarya na jam’iyyar ADC, ya nuna shakku kan ci gaban da gwamnatin ke samu, yana mai bayyana hakan a matsayin tafiyar hawainiya da kuma rashin wadatuwa.

A martanin da ya mayar, Adelabu ya kare gwamnatin kuma ya tabbatar da cewa an samu gagarumin nasarori a ɓangarori da yawa.

A cewar ministan, sabon tashar da aka ƙaddamar zai inganta samar da wutar lantarki ga al’ummomi da suka haɗa da Abaranje, Isijola, Igando Road, Omoboriowo, Okerube, da kewaye a Legas – rage kashe wutar lantarki, tallafawa ƙanana da matsaƙaitan ‘yan kasuwa, da kuma bunƙasa harkokin tattalin arzikin cikin gida.

Ya kuma yaba wa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ikeja, (DisCo) da ke da alhakin kammala aikin a cikin watanni 12, inda ya bayyana kwarewarsu ta fasaha, hada-hadar masu ruwa da tsaki, da kuma yadda ya dace.

Adelabu ya ƙara da cewa, “Ikeja Electric na ɗaya daga cikin manyan kamfanonin DisCos a Nijeriya.

Ministan ya ci gaba da zayyana wasu muhimman nasarori da aka samu kawo yanzu a ƙarƙashin shirin sake fasalin ɓangaren wutar lantarki na Shugaba Tinubu:

ƙaddamar da dokar samar da wutar lantarki ta 2023, wadda ta karkata fannin wutar lantarki, kuma ta kai ga kunna kasuwannin wutar lantarki a matakin jihohi 12 – karo na farko a tarihin Nijeriya.

By ukarofi