
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Ɓangaren jam’iyyar PDP da ke goyon bayan Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, ya sanar da naɗa Kabiru Tanimu Turaki a matsayin shugaban riƙon ƙwarya na ƙasa na jam’iyyar.
An naɗa Turaki ne domin jagorantar kwamitin riƙo mai mambobi 13 a ranar Litinin, yayin taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) karo na 103 da aka gudanar a Abuja, kamar yadda rahotanni suka bayyana.
Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin shugabanci ke addabar jam’iyyar a mataki na ƙasa.
