Daga AISHA ASAS
A ranar 29 ga watan Mayun shekarar 2023 ne Gwamna Dauda Lawal ya karɓi ragamar gwamnati daga hannun gwamnatin da ta gaza biyan hukumomin jarrabawar har tsawon shekaru uku, hakan kuwa ya kawo ci baya tare da dakushe ɗaliban babbar sakandare na faɗin jihar ta Zamfara daga rubuta jarrabawar ƙare sakandare, wato WASSCE DA NECO.
A cikin wata sanarwa da ta fito daga hannun kakakin gwamnan Jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ta bayyana cewa, “daga cikin matsalolin da gwamnatinmu ta gada akwai batun rashin biyan kuɗin tallafin karatu ga ’yan asalin Jihar Zamfara da aka tura karatu a ɓangarorin ilimi daban-daban a ƙasar Cyprus da Indiya.”
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Ga ɗalibanmu na Indiya da Sudan, gwamnatin Jihar Zamfara ta yi matsaya mai kyau tsakaninta da makarantun da ke ɗauke da ɗaliban nata. Yanzu haka dai ‘yan asalin Jihar Zamfara da ke karatu a Indiya sun kammala karatunsu, suna shirin komawa gida.
Sakamakon yaƙin da ake yi a Sudan, an kwashe ’yan asalin Zamfara 66. Duk da haka, 14 daga cikin 66 ɗaliban jinya ba su iya yin jarrabawar ƙarshe ba. Saidai ba mu bari hakan ya zama tasgaro ga karatun nasu ba, domin da haɗin gwiwar jami’ar Sudan, gwamnatin jihar ta shirya jarrabawa ga ɗalibai 14 a Najeriya, inda ta ɗauki nauyin duk abinda hakan ke buƙata. Daga cikin ababen da gwamnati yi don ganin ta cika wa waɗannan ɗalibai nata burinsu, akwai ɗaukar nauyin zuwan malaman su na can ƙasar Sudan ɗin don ganin komai ya tafi daidai da tsarin jami’ar da ta ba su karatun tun farko, ta hanyar biyan kuɗaɗen jirgi, wurin kwana da abinci ga masu jarrabawar uku daga Sudan. Dukkan ɗalibai 14 sun kammala jarrabawar ƙarshe, yayin da wasu 52 suka samu cikakken tallafin karatu a jami’o’i a Najeriya.
Mun jagoranci wannan kingiya akan india da sudan,inda tallafin karatu na zamfara ya jawowa ɗaliban dake ƙarƙashin gwamnatin jiha matsasoli da dama, har wa yau tambaya anan shine me ya sa babbar jami’ar Cyprus ke da bambanci?
Mun gina shirin namu ne ta hanyar yin magana a ƙasashen Indiya da Sudan, inda ɗaliban Zamfara suka fuskanci matsaloli daban-daban da gwamnatin jihar ta haifar masu. Abin tambayar ana shi ne, me ya sa Jami’ar ƙasa da ƙasa ta Cyprus za ta bambanta?”
Duk da tarin matsalolin da aka bankado dangane da gurbataccen shiri da aka yi a lokacin da aka tura ɗalibai zuwa Cyprus da wasu ƙasashe, hakan bai sare wa gwamnatin jihar gwiwa ba, domin bai hana ta yin mai yiwa ba ta hanyar bin dukkanin hanyoyin da za a bi don magance matsalar, sai dai mahukuntan makarantar na daƙile yunƙurin.
A ranar 12 ga Nuwamba, 2023, gwamnatin jihar ta biya jami’ar Naira miliyan 84.7. Bayan kwana biyu, wanda ya yi daidai da ranar 14 ga Nuwamban, aka sake tura wa makarantar da ƙarin Naira miliyan 30.9.
Duk da wannan yunƙi da neman mafita da gwamnatin ke yi, jami’ar ta Cyprus ta ci gaba da yin watsi da buƙatar gwamnatin jihar na aikewa da tawaga don tattauna batutuwan da suka shafi ɗalibanmu na tallafin karatu. Hakan ya sa gwamnatin jihar ta tuntuɓi ofishin jakadancin Najeriya da ke Turkiyya domin neman taimako.
A watan Mayun 2024, bayan gagarumin matsin lamba daga Ofishin Jakadancin Nijeriya na ƙasashen Waje a Turkiyya, hukumomin makarantar sun sanar wa gwamnatin jihar cewa, a shirye suke su karɓi tawagarmu a jami’ar da ke Cyprus.
Dangane da sha’anin kuɗi kuwa, gwamnatin ta sake tura wasu kuɗaɗen a asusun makarantar don ƙara tabbatar mata a shirye take, kuma ta ɗauki lamarin karatun ɗalibanta da muhimmanci, inda a ranar 4 ga Yuni, 2024, gwamnatin ta aika da Naira miliyan 100 kamar yadda jami’ar ta buƙata.
Dangane da haka ne Gwamna Dauda Lawal, ya kafa wata tawaga mai mutane uku domin tafiya jami’ar ƙasa da ƙasa ta Cyprus. Tawagar wadda ta haɗa da Mallam Wadatau Madawaki, kwamishinan ilimi, kimiya da fasaha; Bello Mohammed Auta, kwamishinan kuɗi, da Barau Muazu, mai bawa gwamna shawara na musamman kan harkokin kuɗi da tattalin arziki.
Tawagar na da alhakin tabbatar da haƙiƙanin adadin kuɗaɗen da jami’ar ke bin Jihar Zamfara na daga ɗalibai 93 da aka tura bisa tallafin karatu tun daga shekarar 2019, tantance dukkan ɗaliban na Jihar Zamfara da ke jami’ar, don sanin haƙiƙanin adadinsu ta hanyar ganawa da su, da tabbatar da kwasa-kwasan ɗaliban, tare da auna ƙoƙarin su, da tabbatar da shekarar kammala karatun kowane ɗalibi.
Sauran nauyin da ya rataya kansu sun haɗa da ganowa da tantance yanayin da ake gudanar da karatun, halin da gidajen kwanan ɗalibai suke ciki, ciyarwa da sauran kayan aikin ilmantarwa da samar da ababen more rayuwa, da samar da sharuɗɗa da aka amince da juna ta hanyar da aka kafa fitattun abubuwan da za a bi a nan gaba. a daidaita.
Kafin barin Najeriya, tawagar ta tuntuɓi ofishin jakadancin Najeriya da ke ƙasar Turkiyya, dalilin da ya sa wasu jami’an ofishin guda biyu suka shiga tawagar zuwa ƙasar Cyprus a ranar 14 ga Agusta, 2024 kenan, domin kammala aikin da aka yi a sama. A ranar 15 ga watan Agusta, sun gana da daliban da jami’ar gudanarwar jami’ar.
Ganawar farko da hukumar ta yi ta da Farfesa Majid, wanda tawagar ta buƙaci a aiwatar da duk wata yarjejeniya ta MOU tsakanin Jami’ar da Gwamnatin Jihar Zamfara, jimillar bashin da ake bin kowane ɗalibi, tun daga farko har zuwa yau, takardar sheda da ta nuna adadin kuɗin da ake bi a kowane zangon karatu. Shaidar biyan kuɗi da kuma ragowan bashi na kowane ɗalibi. Jimilar kuɗin kowane zango, tare da hasashen lokacin kammala karatu. Da kuma jerin ɗaliban da suka biya kuɗi da kansu don rajista domin guje wa tsaiko a karatun, da kuma adadin kowane ɗalibi ya biya.
A ganawar da ta yi da shugaban jami’ar Farfesa Habil Nadiri, tawagar ta gabatar da batutuwa da dama da ɗaliban jami’ar ke fuskanta, waɗanda suka haɗa da rashin rajistar ɗalibai domin ba su damar halartar laccoci da kuma samun kayan aikin makaranta don gudanar da karatunsu. Korar ɗaukacin caliban (ban da mata goma daga ciki) waɗanda ke ɗakin kwanan dalibai maza, hana dukkan ɗalibai (har da matan goma) abinci daga kantin makarantar tun ranar da aka kore su daga otel.
