Zamfara: Bayan kwanaki 13 a hannun ƴan bindiga, an ceto mata da ƴaƴan sakataren gwamnati, an kama mutane biyar

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Haɗakar jami’an tsaro a jihar Zamfara ta yi nasar ceto iyalan Sakataren Gwamnatin jihar, Malam Mohammed Abubakar Nakwada bayan shafe kusan sati biyu a hannun ƴan bindiga.

Sadiya Nakwada, A’isha Nakwada da Abubakar Ɗan Fulani ne waɗanda aka yi garkuwa da su a ranar 27 ga Yuli, 2025 a Gusau, babban birnin jihar.

Da ya ke tabbatar da lamarin, mai sharhi kan harkar magance matsalolin tsaro, Zagazola Makama ya ce an yi nasarar ceto mutanen ne a ƙarƙashin aikin haɗaka tsakanin jami’an ƴan sanda da wasu jami’an sirri daga hedikwatar rundunar a Abuja.

A wani rubutu da ya wallafa ta kafar sada zumunta, Makama ya bayyana cewa jami’an sun kai samame ne a maɓoyar ƴan bindigar bayan samun wani bayanin sirri akansa a yankin Ƙauyen Mareri da ke Gundumar Damba a Ƙaramar Hukumar Gusau.

Haka kuma, an kama mutanen biyar da ake zargin su da hannu a aikata laifin ba tare da harbin ko daya daga cikinsu ba, kamar yadda ya wallafa.

Mutanen sune; Hamza Umar, Abubakar Abdullahi, Aisha Umar, Mohammed Ibrahim, da Igeh Mohammed, waɗanda baki ɗayansu ƴan yankin Mareri ne, inda a yanzu suke hannun ƴan sanda yayin da ake gudanar da bincike akan su.

By Babaji