
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Jami’an Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta’annati EFCC, sun kai samame a ‘Green Legacy Hotel’ da ke cikin farfajiyar ɗakin karatu na ƙasa na Olusegun Obasanjo a Abeokuta, Babban Birnin Jihar Ogun.
A yayin haka ne aka kama wasu matasa bisa zargin su da ayyukan damfara ta intanet.
Saidai EFCC ba ta tabbatar da zancen ba a hukumance.
Matasa da dama jami’an suka kama da wasu motoci masu alfarma da kuma wasu ababe masu tsada, kamar yadda NewsPointNigeria ta ruwaito.
An ruwaito cewa a safiyar ranar Lahadi ne jami’an suka ƙaddamar da atisayen a yayin wani ƙaramin taro a farfajiyar ɗakin karatun.
Darakta Manaja na ɗakin karatun, Vitalis Ortese ya tabbatar da aukuwar lamarin, saidai bai bada wani ƙarin bayani akan haka ba.
