
Hukumar Gudanarwar Gasar Nigerian Premier League, NPFL ta ci tarar ƙungiyar Kano Pillars bayan wani hayaniya da ya ɓarke a yayin karawarta da Shooting Stars a mako na 8 da wannan kakar.
Akan haka ne Kano Pillars za ta biya Naira milyan 9.5, sannan za a zaftare mata maki uku da kuma haramta mata wasa a gida saboda rikici.
Hukuncin da aka ɗauka akan Kano Pillars shi ne kamar haka:
- Tarar Naira Miliyan Daya (₦1,000,000.00) saboda rashin samar da isasshen tsaro da inganci.
- Tarar Naira Miliyan Daya (₦1,000,000.00) saboda jefa abubuwa masu hadari zuwa cikin filin wasa da jifan jami’an wasa.
- Tarar Naira Miliyan Daya (₦1,000,000.00) saboda rashin tabbatar da ladabi da doka da magoya bayan kungiyar ke yi.
- Tarar Naira Miliyan Daya (₦1,000,000.00) bisa laifin rashin da’a da ya iya kawo rashin mutunci.
- Tarar Naira miliyan biyu (₦2,000,000.00) saboda cin zarafin ‘yan wasan da sukazo bakuncin wasa da jami’an wasa.
- Tarar Naira Miliyan Biyu (₦2,000,000.00) a matsayin diyya na jiyya da lahani da aka yi wa ‘yan wasan da jami’ai.
- Tarar Naira miliyan daya da dubu dari biyar (₦1,500,000.00) a matsayin diyyar Naira dubu dari biyu da hamsin ga kowanne jami’an wasan.
- Umarnin cire maki 3 ga Kano Pillars saboda cin zarafin jami’an wasan.
- Umurnin rufe filin wasa na Sani Abacha har abada, ga Kano Pillars FC, na sauran kakar wasan bana, ko kuma a kalla rasa buga wasanni goma a gida har sai kun tabbatar da cewa ba za a sake samun qfaruwar haka anan gaba ba.
A halin yanzu, Kano Pillars za ta buga wasanninta na gida a Katsina.

