An sake zaɓar Benjamin da Okonkwo a matsayin shugaba da babban sakataren SWAN

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

A ranar Jumma’a aka kammala babban taron Ƙungiyar Maruwaita Labaran Wasanni ta Ƙasa (SWAN), inda aka sake zaɓa da rantsar da Mista Isaiah Kemje Benjamin (JP) da Amb. Ikenna Okonkwo ANIPR a matsayin shugaba da babban sakatare na wa’adin wasu shekaru uku.

Taron, wanda ya samu halartar wakilai daga jihohi a sassan Nijeriya, ya kuma samar da sabuwar majalisar zartarwar (NEC), wadda aka ɗora wa alhakin kula da harkokin ƙungiyar na tsawon shekaru uku.

Zaɓen, wanda aka gudanar a ranar 28 ga Agusta, 2026, ya bayar dama da kuma fage ga wakilai domin yin nazari akan goben ƙungiyar da kuma zaɓar jami’an da za su jagoranci harkokinta.

Duk da cewa da dama daga cikin muƙaman babu gasa akansu, an samu karawa a muƙaman mataimakin shugaba da mataimakin shugaba na shiyyar Arewa maso Gabas.

Ga jaddawalin zaɓaɓɓun jami’an SWAN, kamar yadda Leadership ta wallafa:
“President: Isaiah Kemje Benjamin (JP)

Deputy President: Nyong Bonny Silas

Secretary General: Ikenna Okonkwo

Deputy Secretary General: Samuel Ahmadu

Treasurer: Amusan Olufemi Ayorinde

Financial Secretary: Ijeoma Nwante

Vice President, North-East: Samuel Gangwaja

Vice President, North-West: Zaharadeen Saleh

Vice President, South-South: Azuka Chiemeka

Vice President, South-East: Ikemefuna Asika

Vice President, South-West: Ayodeji Ogunsakin.”

By Babaji

Leave a Reply