
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
A ranar Juma’a aka tabbatar tare da fitar rukuni guda 12 na wasannin gasar Kofin Duniya na 2026, wanda ƙasashen Amurka, Kanada da Mexico za su jagoranta.
Za a gudanar da wasannin ne daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga Yulin shekarar, kamar yadda jaddawalinsu da aka fitar a Birnin Washington DC ya bayyana.
Kimanin ƙasashe 48 ne za su fafata a gasar, wadda aka faɗaɗa a wannan karo inda masu masauƙin baƙi suke jagorantar rukunonin A, B da D.
Ga jaddawalin rukuni 12 na ƙasashen kamar yadda Blueprint ta ruwaito:
Group A:
Mexico, South Africa, South Korea, Qualifier
Group B:
Canada, Qualifier, Qatar, Switzerland
Group C:
Brazil, Morocco, Haiti, Scotland
Group D:
United States, Paraguay, Australia, Qualifier
Group E:
Germany, Curacao, Ivory Coast, Ecuador
Group F:
Netherlands, Japan, Qualifier, Tunisia
Group G:
Belgium, Egypt, Iran, New Zealand
Group H:
Spain, Cape Verde, Saudi Arabia, Uruguay
Group I:
France, Senegal, Qualifier, Norway
Group J:
Argentina, Algeria, Austria, Jordan
Group K:
Portugal, Qualifier, Uzbekistan, Colombia
Group L:
England, Croatia, Ghana, Panama.
