
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Rahotanni daga Jihar Filato sun bayyana cewa wasu ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗan majalisar dokokin jihar da ke wakiltar mazaɓar Pankshin ta Kudu, Hon. Denty Laven.
A cewar rahotannin, an yi garkuwa da shi ne a gidansa da ke yankin Dong a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.
Jihar Filato na fuskantar ƙalubale a fannin al’amuran tsaro a ƴan kwanakin nan, inda haka ya sa jami’an tsaro suke ta ƙoƙarin shawo kan al’amarin.
A makon da ya gabata ƴan bindiga suka shiga unguwar, inda suka yi garkuwa da ɗan hidimar ƙasa na NYSC da wani ɗalibin Jami’ar Jos.
Al’amarin ya auku ne a lokacin da ƴan bindigar suka kutsa gidan Solomon Dansura da misalin ƙarfe 10 na dare tare da tserewa da matasan baƙin nasa guda biyu.
Saida ba a samu wani bayani daga jami’an gwamnati ko ofishin ƴan sanda ba a yayin kammala rahoton.
