Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, ta tsayar da ranar da za ta gudanar da zaɓen gwamnan da na majalisar tarayya da na jihohi a wuraren da zaɓe bai kammala ba.
INEC ta ce ya zuwa ranar 15 ga Afrilun 2023 za ta gudanar da zaɓe a wuraren da lamarin ya shafa.
Hukumar ta bayyana hakan ne ta shafinta na Tiwita a ranar Litinin.
“Bayan taro da aka yi yau, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta yanke gudanar da dukkan zaɓukan gwamna, na ‘yan majalisar tarayya da na jihohi da suka yi saura a ranar Asabar, 15 ga Afrilun 2023.
“Ƙarin bayani na nan tafe ba da jimawa ba,” in ji sanarwar.